KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 04/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 4 ga watan Maris 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga AIsha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Spain ta mayar da martani kan barazanar Trump saboda adawarta da harin Iran

    ...

    Asalin hoton, RONALD WITTEK/EPA/Shutterstock

    Firaministan ƙasar Spain, Pedro Sánchez, ya mayar da martani kan barazanar da Donald Trump ya yi na katse hulɗar kasuwanci tsakanin ƙasashen biyu, sakamakon adawar Madrid ga harin da aka kai kan Iran.

    A jawabin da ya gabatar ta gidan talabijin a safiyar Laraba, Sánchez ya jadadda matsayar gwamnatinsa ta hana Amurka amfani da filin jirginta domin kai wa Iran hari.

    "Ba za mu goyi bayan yaƙi ba” in ji firaministan.

    Ya yi kira da kada a maimaita “kurakuran da suka gabata”, yana mai nuni da mamayar da aka yi wa Iraq a 2003, wadda ya ce ba ta cimma manufofinta ba, sai ma ta haifar da rashin tsaro da kuma taɓarɓarewar rayuwar jama’a da dama.

    Sánchez ya ce hare-haren kan Iran na iya haifar da irin wannan tasiri a fannin tattalin arziki ga miliyoyin mutane, kuma gwamnatinsa na duba matakan da za ta ɗauka domin rage illa.

    A ranar da ta gabata, Trump ya sha alwashin “katse duk wata hulɗa” da Spain, tare da kiran ƙasar da suna marar daɗi, bayan da Sánchez ya ƙi amincewa Amurka ta yi amfani da sansanonin sojinta da ke Spain wajen kai hari kan Iran.

    Madrid ta bayyana harin a matsayin “tsoma bakin soja da bai da hujja kuma mai haɗari.”

  2. Ministan harkokin wajen Iran ya zargi Trump da wargaza tattaunawar sulhu da gangan

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya zargi tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, da “wargaza tattaunawar sulhu da gangan domin ɓata al'amarin” a wani sabon saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta.

    Araghchi ya ce idan aka ɗauki tattaunawar makaman nukiliya mai sarkakiya tamkar cinikin filaye, tare da yaɗa manyan ƙarya da ke ɓoye gaskiya, ba za a taɓa cimma sakamakon da ake fata ba.

    Ya ƙara da cewa abin da ya biyo baya shi ne wargaza tattaunawar gaba ɗaya ta hanyar amfani da ƙarfi.

    A cewarsa, Trump ya ci amanar diflomasiyya da kuma Amurkawan da suka zaɓe shi.

  3. Amurka ta yi iƙirarin kai hare-hare kusan wurare 2000 a Iran tun bayan fara yaƙi

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta yi ikirarin kai hare-hare kusan wurare dubu biyu a Iran tun bayan ƙaddamar da farmakin haɗin gwiwa da Isra'ila.

    Bataliyar rundunar sojin ƙasar a gabas ta tsakiya da ake kira CENTCOM, ta ce ta yi mummunar ɓarna ga garkuwar tsaron samaniyar Iran da kuma nutsar da jiragen ruwan sojin kasar goma sha bakwai.

    Cikin wata sanarwa ta bidiyo, babban kwamandan bataliyar Admiral Brad Cooper, ya ce sojojin Amurka dubu hamsin ne ke yakin.

    Ya ce Iran ta harba makamai masu linzami sama da ɗari biyar, tare da tura jirage marasa matuƙa sama da dubu biyu.

  4. Isra’ila ta gargaɗi mazauna kudancin Beirut su fice

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar Sojin Isra’ila ta fitar da sanarwar gargaɗi ga fararen hula a wasu sassan kudancin birnin Beirut da su fice daga yankin, yayin da musayar wuta tsakaninta da Hezbollah ke ci gaba.

    Rundunar ta ce mazauna yankin Haret Hreik su fice nan take.

    Mai magana da yawun rundunar, Avichay Adraee, ya bayyana cewa an bayar da wannan umarni ne domin kauce wa haɗarin da ka iya tasowa sakamakon hare-haren da ake shirin kaiwa.

  5. Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka a Qatar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar tsaron ƙasar Qatar ta sanar da cewa Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka a Qatar

    Sanarwar ta ce Gatar ta kaɓo ɗaya daga cikin makaman masu linzami da Iran ɗin ta kai hari da su yayin da kuma ɗayan ya faɗa cikin sansanin sojin Amurka da ke Al Udeid, wanda shi ne mafi girman sansanin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Hukumomin Qatar sun ce na a samu asarar rayuka ba kuma babu wanda ya jikkata sakamakon harin.

  6. An sanar da lokacin yin jana'izar Ayatollah Khamenei

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau ne ake sa ran fara gudanar da taron jana’izar Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a birnin Tehran kamar yadda kafar yaɗa labaran ƙasar ta sanar.

    Kafar ta ruwaito cewa za a fara taron da misalin ƙarfe 18:30 na agogon GMT, kuma shirye-shiryen za su gudana na tsawon kwanaki uku kafin a yi jerin gwanon jana’iza.

    An kashe Khamenei ne lokacin da Amurka da Isra’ila suka kai hari kan Iran a ranar Asabar, lamarin da ya ƙara tsananta rikicin da ke tsakanin ɓangarorin.

    Jaridar The New York Times ta ambato wasu jami’an Iran na cewa ɗan Khamenei wato Mojtaba Khamenei na daga cikin waɗanda ake ganin suna kan gaba wajen maye gurbinsa.

    Rahoton ya nuna cewa za a iya yanke hukunci kan sabon jagoran tun da safiyar yau.

    A wani ɓangare kuma, Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya bayyana cewa duk wanda zai gaji Khamenei kuma ya ci gaba da abin da ya kira shirin rusa Isra’ila ko barazana ga Amurka, tare da danne al’ummar Iran, 'za mu kashe shi.”

  7. Me ya sa Amurka da Isra'ila suka kai wa Iran hari, kuma yaushe yaƙin zai ƙare?

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rikici ya ɓarke a Gabas ta Tsakiya bayan kashe jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei, a wasu hare-haren da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar.

    Bayan harin, shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci al'ummar Iran su tuntsurar da gwamnati.

    A matsayin martani, Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a wurare da dama na yankin, kamar ƙasashen Isra'ila da Bahrain da Kuwait da Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da Jordan da Saudiyya da tsibirin Cyprus, har ma da jiragen dakon man fetur da ke ratsawa ta mashigar Hormuz.

    Haka nan ma ƙungiyar Hezbollah mai samun goyon bayan Iran da ke a Lebanon ta shiga faɗan, inda ta harba rokoki zuwa cikin Isra'ila daga sansanoninta da ke cikin Lebanon.

    Isra'ila ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan cibiyoyin Hezbollah a Lebanon.

  8. Yadda kisan Ali Khamenei zai shafi ƴan Shi'a a Najeriya

    ....

    Asalin hoton, JNIM

    Har yanzu duniya na ci gaba da alhinin kisan jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai kan Iran.

    Ayatollah mai shekara 86 na da matuƙar tasiri a Iran da ma ƙasashen duniya, musamman tsakanin mabiya aƙidar Shi'a a faɗin duniya

    Tuni dai mabiya ƙungiyar ƴan'uwa Musulmi a Najeriya ta ,yan Shi'a suka shiga jimaminsa ta hanayr gudanar da taron muzaharori da zanga-zangar lumana domin bayyana alhininsu.

    Malam Sidi Mannir Mainasara ɗaya daga cikin manyan almajiran Sheikh Alzakzaky kuma wanda ya san rayuwar Ayatoullah Ali Khamenei, ya bayyana wa BBC yadda mabiya shi'a a faɗin duniya suka ji da rashinsa.

    Ya ce kisan Ayatollah ya ƙara fito da martaba da tasirin aƙidar Shi'a ke da shi a Najeriya.

    ''Za ka sha mamaki idan ka ga yadda mutane suka ajiye bambancin aƙida suka riƙa yi mana ta'aziyyar rasuwarsa'', in ji shi.

    Ya ci gaba da cewa abin ya ba su mamaki, yadda mutuwarsa ta mantar da al'umma bambancin aƙida.

  9. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.