Coronavirus a Afrika Ta Kudu: An bukaci gwamnati ta sake haramta sayar da giya

Malema

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Mr Malema ya ce za a dora alhakin mace-macen da ke da alaka da shan barasa a kan Shugaba Ramaposa

Shugaban hamayya na Afrika Ta Kudu Julius Malema ya yi kira ga gwamnati da ta dawo da haramcin da ta sanya kan barasa a lokacin kullen cutar korona.

Shugaban jam'iyyar Economic Freedom Fighters (EFF), yana caccakar matakin Shugaba Cyril Ramaphosa ne na bude harkokin kasuwanci a wani jawabi da ya gabatar na murnar Ranar Matasa Ta Afrika Ta Kudu.

Afrika Ta Kudu ta shafe wata biyu cikin kullen cutar korona mafi tsauri a duniya - inda har aka dakatar da sayar da giya.

Ana ganin matakin zai rage cin zarafi da ke faruwa a gidajen aure, da hana tashe-tahsen hankula da kuma saukaka wa asibitoci yanayin da suke ciki a lokacin kulle.

An alakanta yawan aikata laifuka da dage haramcin sayar da giyar da aka yi a ranar 1 ga watan Yuni.

"Mun yi kira da a sake duba dage haramcin sayar da barsa, don kare rayuwar al'umma fiye da ribar da za a samu,'' kamar yadda Malema ya fada aranar Talata.

"Shugaban kasa da kansa ya bari a sayar da giya a kasar da take da tarihin yawan mace-mace da samun marasa lafiya sakamakon rikice-rikicen da shan barasa ke jawowa.''

Mr Malema ya ce za a dora alhakin mace-macen da ke da alaka da shan barasa a kan Shugaba Ramaposa ya kuma zargi shugaban da zama abokan Turawan da suka mamaye tare da juya ragamar kasar.''

Shugaban jam'iyyar ta EFF a baya ya nuna adawa da sake bude makarantu da wuraren ibada da aka yi.

Afrika Ta Kudu ta sake bude makarantu ne ga daliban shekarar karshe a ranar 8 ga watan Yuni, amma tuni aka sake rufe makarantu da dama da a baya aka bude bayan samun karuwar masu dauke da cutar korona.