Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Coronavirus: Mara lafiya ya tsere daga asibiti
Ma'aikatar lafiya a Zimbabwe ta tabbatar da cewa wani mutum da ake zargin yana dauke da coronavirus ya tsere daga asibiti kafin a yi masa gwaji.
Cikin wata sanarwa, ma'aikatar ta ce mutumin mai shekara 26 ya shiga kasar a watan Fabrairu daga Thailand kuma ya fara zazzabi da atishawa.
A cewar sanarwar, bayan da mutumin ya tsere an bi shi gidansa don kamo shi amma ba a yi nasara ba kuma an bukaci jami'an 'yan sanda su nemo shi.
Kawo yanzu dai, alkaluma sun nuna cewa an samu masu dauke da cutar 100 a fadin Afirka.
Su ne:
- Masar - 55
- Algeria - 20
- Afirka ta Kudu - 7
- Tunisia - 5
- Senegal - 4
- Maroko - 2
- Kamaru - 2
- Burkina Faso - 2
- Najeriya - 2
- Togo - 1
Masar ce kasar da ta fi samun yawan masu dauke da cutar a nnahiyar Afirka.
Kawo yanzu a fadin duniya cutar ta kama kusan mutum 100,000 kuma ta kashe sama da 3,000 a China kawai.
Cutar ta billa a manyan kasashen duniya kamar Amurka da Burtaniya da Italiya.