Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
'Har yanzu APC ba ta cika jam'iyya ba'
Jam'iyya mai mulki a Najeriya ta APC ta kasance cikin rikici tun bayan da aka kammala manyan zabukan watan Fabarairun 2019 a kasar.
Rashin jituwa tsakanin wasu gwamnoni da kuma shugabancin jam'iyyar na kasa karkashin Adams Oshiomole ya janyo rarrabuwar kai tsakanin jiga-jigan jam'iyyar.
Wannan ta sa masharhanta irinsu Dakta Abubakar Umar Kari na Jami'ar Abuja ke ganin har yanzu "APC ba ta zama cikakkiyar jam'iyya ba".
Ko a ranar Asabar rahotanni sun ambato kungiyar gwamnonin APC tana kiran kwamitin gudanarwar jam'iyyar na kasa da ya sauke Oshiomole daga mukaminsa, inda suka goyi bayan hukuncin wata kotu a Abuja.
A ranar Larana ne wata kotu a Abuja ta yanke hukuncin korar Adams Oshiomole daga mukaminsa na shugaban jam'iyyar ta APC na kasa.
Wannan ya biyo bayan karar da wasu suka shigar cewa tuni aka dakatar da Mista Oshiomhole daga jam'iyyar APC a jiharsa ta Edo, abin da alkalin ya dogara da shi kuma ke nan yayin bayar da hukuncin.
Sai dai a daukaka karar da ya yi, wata kotu a Jihar Kano ta yi umarni da Oshiomhole ya ci gaba da zama a mukaminsa har sai bayan ta yi hukunci.
'Har yanzu ba ta zama cikakkiyar jam'iyya ba'
"Muna fada muna nanatawa cewa har yanzu APC ba ta zama cikakkiyar jam'iyya ba, gungu-gungu ne na mutane da ke da akidu daban-daban wadanda a baya ma fada suke yi da juna," in ji Dakta Abubakar Umar Kari, masanin kimiyyar siyasa a Jami'ar Abuja.
Ya kara da cewa abin da kawai ya hada 'yan jam'iyyar APC shi ne "wata dama da za su karbi mulki a shekarar 2015".
Jam'iyyar APC dai ta kafu ne bayan jam'iyyun AC da CPC da ANPP da wani bangare na APGA sun dunkule kafin a shiga babban zaben 2015, abin da ya sa suka kwace mulki daga hannun jam'iyyar PDP da dan takararta Shugaba Goodluck Jonathan.
"Idan irin wannan rikici ya ci gaba abubuwa da dama za su iya faruwa da ita (APC), wadansu ma na ganin za ta iya wargajewa," Kari ya fada.
"Ko da haka ba ta faru ba to ina ganin kwarjininta zai ragu kwarai da gaske."
Dakta Kari ya ce tabbas a siyasa ba a rasa yadda za a yi wurin gyara matsaloli, sai dai yana ganin cewa halin ko-in-kula na Shugaba Buhari a matsayinsa na jagora zai iya kawo tsaiko wurin saita jam'iyyar.
"Shugaba Muhammadu yana da hailin ko-in-kula, ba shi da niyyar a sasanta, ba ya wani katabus, kuma ba abin mamaki ba ne idan halin nasa ya ci gaba."