Wasu 'yan Najeriya sun kai wa Amaechi hari a Madrid

Ministan sufurin Najeriya Rotimi Amaechi

Asalin hoton, @ChibuikeAmaechi

Lokacin karatu: Minti 1

Ministan sufurin Najeriya Rotimi Amaechi ya ce wasu 'yan Najeriya sun kai masa hari a birnin Madrid.

Sakon da ya wallafa a Twitter, tsohon gwamnan na Rivers ya ce an kai masa harin ne yayin da yake halartar taron sauyin yanayi da ake gudanarwa a birnin Madrid na Spain.

Ya ce 'yan sandan Madrid ne suka tarwatsa 'yan Najeriya kafin su yi masa rauni.

"Ban ji rauni ba, na gode da goyon bayanku da kuma addu'arku," kamar yadda ministan ya wallafa a Twitter.

Kauce wa X, 1
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 1

Bidiyon yadda 'yan Najeriyar suka kai wa ministan hari ya mamaye kafofin sada zumunta na intanet.

Kauce wa X, 2
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 2

Wasu jaridun Najeriya sun ambato kungiyar IPOB da ke fafutikar kafa kasar Biafra tana ikirarin cewa mambobinta ne suka kai wa Amaechi hari a Spain.

Kuma kungiyar ta ce za ta ci gaba da kai 'yan siyasa hari a duk lokacin da suka yi katari da su a kasashen duniya.