Me doka ta ce kan barawon akwatin zabe?

Asalin hoton, Getty Images
Tun bayan da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa duk wanda ya saci akwatin zabe ya yi a bakin ransa, 'yan kasar suke ta cece-kuce a kan wannan kalamai na sa.
A wannan dalili ne ya sa BBC ta tuntubi wani lauya a Najeriya watau Dakta Aminu Gamawa, a kan ko me doka ta ce a kan wanda ya saci akwati.
Dakta Aminu dai ya bayyana cewa dokar kasar ta hana sace akwatin zabe kuma duk wanda aka samu da laifin yin hakan, za a iya yanke masa hukuncin zaman gidan yari na kusan shekaru biyu.
Ya bayyana cewa idan aka kama barawon akwatin zabe, jami'an tsaro su kamashi su bincike shi sa'annan a gurfanar dashi gaban kotu.
Ku latsa hoton da ke sama don sauraron hirar Barista Aminu Gamawa.
Lauyan ya kuma ce bai kamata a ce idan an kama barawon akwatin ba an dauki doka a hannu, ya ce kotu ce kadai ke da hurumin hukunta shi.
An dade ana fama da batun satar akwatin zabe a Najeriya a lokacin zabe inda ake samun 'yan barandan siyasa suna irin wannan aika-aika.
Tuni dai wasu manya a jam`iyyar APC suka ce shugaban kasar gargadi ne kawai yake yi.
inda suka ce jama'a da dama sun jahilci kalaman na shugaban kasa.
Babbar jam`iyyar hamayyar kasar dai, wato PDP ta yi zargin cewa shugaban kasar na so ne ya yi amfani da jami`an tsaro wajen dakile `yan adawa.
An fara wallafa labarin ranar 19 ga watan Fabrairu.











