Shin EFCC ta kama alkalin alkalan Najeriya Walter Onnoghen?

Alkalin alkalan Najeriya sharia Walter Onnoghen

Asalin hoton, @Crevo360_Ng

Lokacin karatu: Minti 2

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta'annati, EFCC, ta musanta rahotannin da ke cewa ta kama alkalin alkalan kasar Walter Onnoghen.

Ana tuhumar mai shari'a Onnoghen da zargin yin karya wajen bayyana kaddarorin da ya mallaka.

A ranar Litinin ne kotun da'ar ma'aikata ta soma sauraren tuhumar da ake yi masa, ko da yake bai gurfana a gabanta ba saboda, a cewar lauyoyinsa, ba a mika masa sammaci ta hanyar da ta dace ba.

Sai dai wasu rahotanni sun ambato EFCC na cewa ta kai samame gidan alkalin alkalan na Najeriya inda ta yi awon gaba da shi.

Amma a sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter ta musanta labarin, tana mai cewa labarin karya ne.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

"An jawo hankalin EFCC kan labarin karya da ake watsa wa a shafukan sada zumunta cewa EFCC ta kama alkalin alkalan Najeriya, Mai shari'a Walter Onnoghen.

Wannan ba komai ba ne face zugitamalle daga wurin masu yada labaran karya. Muna so a sani cewa EFCC ba ta je gidan alkalin alkalai domin ta kama shi ba kuma ba ta aike masa da gayyata a game d hakan ba."

Abin da ya sa aka dabe shari'ar Walter Onnoghen

Bayanan bidiyo, Kotun da'ar ma'aikata da ke Abuja

Kotun da'ar ma'aikata ta dage zamanta na sauraron shari'ar da ake yi wa Alkalin Alkalan na Najeriya Mai shari'a Walter Onnoghen, bayan ya ki bayyana a gaban kotun a ranar Litinin.

Laifuka shida ne ake tuhumar babban alkalin, dukkanninsu sun shafi kin bayyana dukiyar da ya mallaka.

Sai dai babban alkalin ya tura wasu manyan lauyoyi 47 wadanda suka wakilce shi.

Lauyoyin babban alkalin sun ce bai bayyana ba ne saboda ba a mika wa mutumin da suke karewa takardar sammaci a hannunsa ba.

Sun kara da cewa kotun ba ta da hurumin sauraren shari'ar.

Daga nan ne kotun ta dage zamanta har zuwa ranar Talata 22 ga watan Janairun.

Mukaddashin mai shari'a na Nigeria Walter Onnoghen

Asalin hoton, Nigerian Government