Ngozi Okonjo-Iweala ta zama darakta a kamfanin Twitter

Asalin hoton, Getty Images
Kamfanin sada zumunta na Twitter ya nada tsohuwar Ministar Kudin Najeriya Ngozi Okonjo-Iweala a matsayin daya daga cikin daraktocinsa.
Kamfanin wanda yake da hedkwata a jihar California ta kasar Amurka ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis.
Misis Okonjo-Iweala ita ce mace ta farko da ta fara zama ministar kudin kasar da kuma ministar harkokin waje a tsakanin shekarun 2003 zuwa 2006.
Har ila yau ta kara sake zama ministar kudin kasar kuma mai kula da harkokin tattalin arziki a zamanin mulkin Shugaba Goodluck Jonathan.
Shugaban kamfanin Omid Kordestani ya ce yana yi wa Misis Okonjo-Iweala da Mista Robert Zoellick, wanda shi ma kamfanin ya dauke shi aiki a matsayin darakta, maraba kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Twitter.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Ita ma Okonjo-Iweala ta bayyana farin cikinta da sabon matsayin, kamar yadda ta bayyana a shafinta na Twitter.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Tsohuwar ministar ta taba yin aiki da bankin duniya, inda ta shafe fiye da shekara 20 a hedkwatarsa da ke birnin New York na Amurka.
Karanta wadansu karin labarai











