Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
An kai wadda ake zargi da kashe mijinta gidan yari a Abuja
- Marubuci, Abdulwasiu Hassan
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja
Matar da ake zargi da kashe mijinta, Maryam Sanda, ta bayyana a gaban wata babbar kotu da ke Abuja ranar Juma'a.
Ana zargin ta ne da kashe mai gidanta, Bilyaminu Bello, bayan ta daba masa kwalba a sassan jikinsa.
Al'amarin ya faru ne a gidan ma'auratan da ke unguwar Wuse a Abuja.
Lauya mai shigar da kara ya ce suna so su sauya tuhume-tuhume saboda sabbin hujjoji da aka samu sakamakon bincken da ake yi mata.
Maryam ta shiga kotun ne tana rungume da jaririyarta da kuma Al-Kur'ani a hannunta, inda ta lullube fuskarta ba a iya gani.
An karanta mata tuhume-tuhume da ake mata.
Ana tuhumurta da daba wa mijinta fasasshiyar kwalba a kirji wanda ya yi sanadin mutuwarsa, amma ta musanta hakan tana mai zubar da hawaye.
Tuhuma ta biyu an ce ta ji masa ciwo da kwalba a kirji wanda ya yi sanadin mutuwarsa, a nan ma Maryam ba ta amsa yin laifin ba.
Lauya mai kare wadda ake kara ya ce ba sa sukar dage zaman shari'ar sai dai suna so a ba da wadda ake zargi beli.
Kotun dai ta bayar da umarni a atsare ta a gidan yari na Suleja.
Daga nan ne Alkalin Kotun Yusuf Halilu ya dage zaman shari'ar zuwa ranar 7 ga watan Disamba.