Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Saudiya za ta gina birnin nishadi a kusa da Riyadh
Saudiya ta na shirin gina abin da ta bayyana a matsayin birnin nishadi a wajen babban birnin kasar, Riyadh.
A shekarar 2022 ake sa ran bude birnin, a inda za a rinka bukukuwan baje kolin al'adu, da wasanni da kuma abubuwan shakatawa.
Mataimakin yarima mai jiran gado a Saudiya, Mohammed bin Salman ya ce ana fatan birnin da za a gina, zai zama wani wuri mai muhimmanci ga raya al'adu da cimma bukatun mutane masu tasowa a kasar a gaba.
Gwamnatin Saudiya na fatan wannan shiri da ake wa lakabi da Vision 2030, zai samar da guraben ayyukan yi ga matasa a kasar, tare da yin sassauci ga wasu tsauraran ka'idoji a kasar.