Robertson zai bar Liverpool a karshen kakar bana, Liverpool
Andy Robertson zai bar Liverpool FC a ƙarshen kakar wasa bana, bayan kwantiraginsa ya ƙare, kamar yadda ƙungiyar ta sanar.
Robertson mai shekaru 32 ya koma Liverpool daga Hull City a shekarar 2017 kan kuɗi fam miliyan 8, kuma ya lashe kofunan Premier League biyu da UEFA Champions League Merseyside.
Robertson ɗaya ne daga cikin ƴan wasan da Tottenham ke son siya a a watan Janairu, amma ba su kai ga cimma matsaya ba.
Sai dai Liverpool ta kasa kammala cinikin ne saboda ba ta iya dawo da Kostas Tsimikas daga aron da yake yi a AS Roma ba.
A wannan kakar, damar Robertson ta buga wa Liverpool wasanni ta ragu karkashin kocin Arne Slot, musamman bayan zuwan ɗan wasa Milos Kerkez wanda ya koma Liverpool daga AFC Bournemouth kan kwantiragi fam miliyan 40.
Ya buga wasa 373 a Liverpool kuma ya lashe jimillar kofuna tara yayin da yake taka leda a Anfield.