An mayar da ƴan gudun hjirar Najeriya 153 gida daga Nijar
Najeriya ta karɓi ƴan gudun hijirar ƙasar 153 daga Jamhuriyar Nijar a wani yunkuri na tabbatar da dawowarsu cikin aminci da daraja.
Ofishin hukumar ba da agajin gaggawa ta NEMA reshen Kano ne ya karɓi waɗannan ƴan gudun hijira tare da haɗin gwiwar Hukumar ƴan gudun hijira ta ƙasa NRC da hukumar ba da agajin gaggawa ta SEMA, da rundunar tsaro ta NSCDC.
Ƴan gudun hijirar sun isa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da misalin ƙarfe 12:50 na tsakar daren Talata ta jirgin Sky Mali Airline.
Bayan kammala rajista da hukumar shige da fice ta Najeriya NIS, an kai su makarantar horarwar hukumar domin gudanar da cikakken bincike da tantancesu tare da dukkan masu ruwa da tsaki.
An gudanar da tantancewar a ranar 27 ga Janairu, 2026, inda bayanan ƴan gudun hijirar suka nuna cewa akwai maza manya 46, mata manya 37, yara maza 38 da kuma yara mata 32.
Hadin gwiwar duk masu ruwa da tsaki ya tabbatar da cewa aikin tantancewa ya gudana cikin tsari, nasara, kuma ba tare da wani matsala mai hatsari ba.