Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 12/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 12 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

DagaHaruna Kakangi da Aisha Babangida da Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Wakiliyar MDD ta isa birnin Goma na Jamhuriyar Dimokraɗiyar Kongo

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai riƙon muƙamin shugabancin shirin daidaita lamurra na Majalisar ɗinkin duniya a Jamhuriyar dimokraɗiyyar Kongo ta isa birnin Goma da ke gabashin ƙasar, wanda ke hannun ƴan tawaye.

    Majalisar ɗinkin duniyar ta ce isar Vivian van de Perre filin jirgin saman Goma, wani mataki ne mai muhimmanci, bayan shafe lokaci mai tsawo jiragen sama ba sa samun damar shiga sararin samaniyar yankin.

    Wakilin BBC ya rawaito cewa Vivian na fatan saukar ta a filin jirgin zai bayar da damar sake buɗe shi sannu a hankali, domin ya amfani mutanen yankin.

    Ƴan tawayen M23 masu samun goyon bayan Rwanda sun dakatar da ayyuka a filin jirgin saman a watan Janairun bara, bayan ƙwace ikon yankin arewacin Kivu mai cike da albarkatun ƙasa, a wani hari da suka kai da ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane.

    Majalisar ɗinkin duniya ta ce ziyarar na da nufin tallafawa shirye shiryen tabbatar da tsagaita wuta, bayan yarjejeniyar zaman lafiya da Rwanda da Congo suka sanya wa hannu a Washington.

  2. Jiragen ruwan sojojin ruwan Amurka sun yi karo da juna a kusa da Kudancin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka da ke yankin kudancin Amurka ta tabbatar wa BBC cewa wani jirgin ruwan yaƙin sojin ruwan Amurka ya yi karo da wani jirgin ruwan da ke samar da man fetur a lokacin da suke aikin samar da mai.

    An bayar da rahoton cewa mutane biyu sun ji ƙananan raunuka yayin aikin da suke gudanarwa a teku kuma \a halin yanzu suna samu kula a asibiti in ji rundunar sojin.

    Jiragen ruwan biyu duk sun ci gaba gudanar da ayyukansu a cikin tekun bayan aukuwar lamarin.

    Rundunar dai ba ta bayyana abin da ya haddasa hatsarin ba, kuma ta ce a halin yanzu ana gudanar da bincike kan lamarin.

  3. 'Za mu kawo ƙarshen aikin yaƙi da baƙin haure a Minnesota'

    ...

    Jami’in kula da kan iyakar Amurka Tom Homan ya ce za a kawo karshen aikin tabbatar da shige da fice a Minnesota, inda ya ce shugaba Donald Trump ya amince da bukatar kawo karshen aikin.

    "Zan kuma ci gaba da zama a Minnesota na ɗan wani lokaci don sa ido na ganin karshen aikin, domin kuma tabbatar da cewa an samu nasara," in ji Homan yayin tattaunawa da manema labarai a safiyar Alhamis.

    Homan ya ce yanzu an rage “ɓata-gari” a Minnesota tun da jami'an yankin sun bai wa jami’an shige da fice na tarayya haɗin kai.

    Aika jami'an shige da fice sama da 2,000 zuwa jihar ya janyo zanga-zanga a faɗin ƙasar, bayan da jami’ai suka kashe wasu ƴan ƙasar biyu a watan da ya gabata.

  4. Za a sake buɗe iyakar Kenya da Somaliya bayan kusan shekara 15

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Kenya William Ruto ya sanar da cewa, za a sake buɗe kan iyakar Kenya da Somaliya a cikin watan Afrilu kusan shekaru 15 bayan rufe ta saboda hare-haren da ƙungiyar al-Shabab ta kai.

    Ƙungiyar da ke da hedkwata a Somaliya, ta kitsa wasu munanan hare-hare a ƙasar Kenya da suka haɗa da wanda aka kai a wata cibiyar kasuwanci a Nairobi babban birnin ƙasar, inda aka kashe mutum 67 a shekara ta 2013, ɗaya kuma a wata jami'a a Garissa shekaru biyu bayan haka inda aka kashe mutum 148.

    Tun da farko an sanar da shirin, a cikin 2023, amma wasu hare-hare sun jinkirta aiwatar da shirye-shiryen.

    Ruto ya ce aniyar sake buɗe mashigar ya biyo bayan aikin tantancewa ta tsaro da aka kwashe shekaru ana yi, inda ya ƙara da cewa za a jibge jami’an tsaro da dama a kan iyakar domin tabbatar da cewa matakin bai kawo cikas ga tsaro ba.

  5. Guguwa ta kashe aƙalla mutum 35 a Madagascar

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Aƙalla mutun 35 ne suka mutu bayan da wata guguwa mai ƙarfin gaske ta afka wa Madagascar, a cewar hukumar taƙaita afkuwar bala'o'i ta ƙasar.

    Guguwar mai suna Gezani ta afka ne ranar Talata, inda ta lalata abubuwa a tashar jiragen ruwa da ke Toamasina.

    Ofishin takaita afkuwar bala'i ta Madagascar ta ce an samu "gagarumin ruɗani" - tare da ruwaito faɗuwar gidaje a yankin da kuma gano gawawwaki.

    Al'ummomi sun shiga cikin duhu sakamakon katsewar lantarki, yayin da itatuwa suka yi ta tuge wa suna faɗi ƙasa.

    Mutane sama da 250,000 ne lamarin ya shafa ko kuma ya ɗaiɗaita, a cewar ministan kula da muhalli ta ƙasar Max Fontaine yayin tattaunawa da BBC.

  6. Ana ci gaba da ƙirga ƙuri'u a zaɓen Bangladesh

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Ana ci gaba da ƙirgan ƙuri'u a Bangladesh, bayan kammala zaɓe na farko tun bayan zanga zangar da ɗalibai suka jagoranta da ta kifar da gwamnatin Firaminista Sheikh Hasina watanni goma sha takwas da suka gabata.

    Gudanar da zaɓen na nuna cika alƙawarin da shugaban riƙo na Bangladesh Muhammad Yunus ya ɗauka na gudanar da zaɓe mai cike da gaskiya da adalci.

    Sai dai jamiyyar Awami League ta Sheikh Hasina ta nuna rashin amincewarta da zaɓen bayan an haramta mata shigar sa.

    Zaɓen zai fi zafi ne tsakanin jamiyyar Jamaat e Islami da ta Bangaldesh Nationalist party.

    Kuma jami'yyun biyu sun yi alƙawarin amincewa da sakamakon zaɓen, idan har sun amince da sahihancinsa.

  7. Gwamnan jihar Sokoto ya bayar da umarnin biyan ma'aikata albashi saboda azumi

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu

    Asalin hoton, FB/Ahmed Aliyu

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya bayar da umarnin biyan ma'aikatan jihar albashin watan Fabarairu nan take, saboda ƙaratowar watan azumin Ramadana.

    Aliyu ya sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa ta hannun shugaban sashen yada labarai da hulɗa da jama'a na ofishin gwamnan, Abubakar Bawa a yau Alhamis.

    Sanarwar ta ce matakin ya shafi: "ma’aikatan Gwamnatin jiha, ƙananan hukumomi, ma’aikatan hukumar Ilimi ta ƙananan hukumomi, da kuma tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a faɗin jihar".

    Bayanin ya ƙara da cewa matakin fara biyan albashin zai fara aiki ne daga ranar Juma'a 13 ga watan na Fabarairu.

    A ranar 18 ko 19 ga watan Fabarairun nan ne ake sa ran al'ummar Musulumi na duniya za su fara azumin watan Ramadana.

  8. 'An ƙwace fasfon tafiye-tafiyen El-Rufa'i'

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai

    Asalin hoton, X/Nasir El-Rufai

    Bayanan hoto, Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai

    Bayanai sun ce jami'an tsaro a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja, babban birnin Najeriya sun ƙwace takardar tafiye-tafiyen tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i, jim kaɗan bayan saukar sa a Najeriya daga ƙasar Masar.

    Sanarwar da mai taimaka wa tsohon gwamnan kan yada labarai Muyiwa Adekeye ya wallafa a shafinsa na X, ta ce "A yau jami'an tsaro sun so su kama Nasir El-Rufai bayan komawarsa gida daga birnin Cairo.

    Ya ci gaba da cewa "El-Rafai ya ƙi bin su ba tare da an nuna masa takardar gayyata ba a hukumance, sai dai duk da haka sun ƙwace takardar fasfo dinsa daga hannun wani mai taimaka masa."

    Wani bidiyo a shafukan sada zumunta ya nuna yadda tsohon gwamnan ke magana da wasu mutane a filin jirgin, inda yake cewa "idan kuna son ku gayyace ni ku ba ni takardar gayyata."

    Nasir El-Rufai

    Asalin hoton, X/Imran Wakili

    Nasir El-Rufai wanda tsohon gwamnan jihar Kaduna ne na cikin jagororin adawa a Najeriya wadanda suka dunƙule a jam'iyyar ADC domin ƙalubalantar shugaba mai ci Bola Tinubu a babban zaɓen ƙasar da za a yi a shekara mai zuwa.

    Cikin makon, a wata tattaunawa da BBC, El-Rufai ya zargi gwamnatin jam'iyyar APC da yi wa ƴan adawar da suka ƙi sauya sheƙa zuwa jam'iyyar barazana ta hanyar kama su da sunan bincike kan ayyukan rashawa.

    “An kama mutum wajen guda huɗu waɗanda muka yi aiki da su a Kaduna, saboda haka ni ma lokaci ne, ni ma za a neme ni,” in ji El-Rufa'i a tattaunawar tasa da BBC.

  9. FRSC ta sallami jami’ai 43 kan nuna ɗabi'u mara kyau

    ....

    Asalin hoton, FRSC

    Hukumar kiyaye afkuwar haɗura ta ƙasa FRSC ta ɗauki matakin ladabtarwa mai tsauri inda ta sallami jami’ai 43 daga aiki sakamakon rashin biyayya da ɗabi’a maras kyau, wanda laifuka ne da suka aikata yayin aiki.

    Sanawar da hukumar ta fitar ta ce "Daga cikin waɗannan jami’an, 31 an sallame su ne saboda rashin biyayya, 5 saboda ɗabi’a maras kyau, sannan 7 saboda aikata laifuka yayin sintiri."

    Shugaban FRSC, Shehu Mohammed ya bayyana wannan mataki a matsayin abu da aka yi don tabbatar da cewa jami'ai sun bi ƙa’idar aiki yadda ya kamata.

    Ya ce "alamar FRSC alama ce ta ɗabi’a da ɗawainiya, kuma kowane jami’in da ya saba wa ƙa’idojin hukumar zai fuskanci hukunci."

    Ya ƙara da cewa rashin biyayya babban laifi ne musamman ga hukumar da aka ɗora wa alhakin kare rayukan mutane a hanyoyi, yayin da ɗabi’a mara kyau da aikata laifuka yayin sintiri ke rage amincin jama’a gare su da kuma sabɓa wa ka’idojin hukumar da suka haɗa da gaskiya da ladabi.

    Hukumar ta ce za ta ci gaba da ƙara lura da ayyukan cikin gida da karfafa tsarin kulawa, da kuma wayar da kan jami’ai kan ɗabi’a mai kyau a dukkan sassan hukumar a faɗin ƙasa.

  10. Tashin hankali ya ƙaru a yankin Amhara na Habasha

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tashin hankali ya ƙaru a yankin Amhara na ƙasar Habasha bayan rahotannin arangama tsakanin ‘yan tawayen Fano da dakarun gwamnati a ɗaya daga cikin manyan garuruwan yankin a ranar Laraba.

    Shaidu sun ce ‘yan tawayen sun buɗe wuta kan sojojin gwamnati a garin Debre Tabor, inda mazauna suka shaida cewa rikicin ya fara ne da safe kuma ya ci gaba har tsawon yini.

    Rahotanni sun ce wasu cibiyoyin gwamnati sun lalace yayin artabun, yayin da ofishin tsaron gwamnatin yankin Amhara ya tabbatar da faruwar rikicin tare da zargin ‘yan tawayen da ƙona kadarorin jama’a.

    Mazauna garin sun kuma ce sun ji ƙarar harbe-harbe masu ƙarfi tare da zargin an kai hare-haren jirage marasa matuƙa, duk da cewa ba a tabbatar da hakan ba daga majiyoyi masu zaman kansu.

    Majiyoyi na kusa da ‘yan tawayen sun ce mayaƙansu sun fice daga garin da yammacin ranar, amma sun yi ikirarin cewa har yanzu suna iko da yankunan.

    Har yanzu ba a san adadin waɗanda suka mutu ko girman ɓarnar da aka yi ba, sakamakon katsewar hanyoyin sadarwa da kuma ƙarancin rahotanni masu zaman kansu daga yankin rikicin.

  11. APC da NNPP sun soki ƙudurin Majalisar Amurka kan 'musguna wa Kiristoci a Najeriya'

    ...

    Asalin hoton, BBC Collage

    Jam'iyyun siyasa biyu a Najeriya sun mayar da martani kan matakin wasu ƴan majalisar wakilan Amurka na gabatar da ƙudurin neman a dauki mataki kan Najeriya bisa zargin musguna wa Kiristoci.

    Ƙudurin ya nemi a sanya takunkumin hana da kuma riƙe kadarorin tsohon ministan tsaro na ƙasar Rabi'u Kwankwaso da kuma ƙungiyoyi biyu na makiyaya a ƙasar.

    Jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar da kuma NNPP mai adawa duk sun soki lamirin ƙudurin.

    Mai magana da yawun jam'iyyar APC, Bala Ibrahim ya ce "bai kamata a yi amfani da shaci-fadi wajen ƙaƙaba takunkumi kan ƴancin zirga-zirga na wani mutum ba ba tare da ji daga gare shi ba.

    "Ina ganin wannan abu ne da bai kamata ba," in ji Bala.

    Ita kuma jam'iyyar NNPP ta musanta cewa Kwankwaso ya take hakkin yin addini duk da cewa a lokacin mulkinsa ne aka amince da amfani da shari'ar Musulunci a jihar a shekara ta 2000.

    A wata ganawa da manema labarai, mai magana da yawun jam'iyyar NNPP na ƙasa Ladipo Johnson ya ce "me ya sa ba a zargi sauran gwamnonin da jihohinsu suka amince da shari'a ba?".

    A ranar Laraba ne wasu ƴan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da wani ƙuduri a majalisar na neman ɗaukar matakai kan Najeriya domin daƙile zargin musguna wa Kiristoci.

    Najeriya ta sha musanta cewa ana kai wa Kiristoci hari kawai sanadiyyar addininsu, inda ta ce "matsalar tsaro ta ƙasar ta shafi kowa ba tare da bambancin addini ba."

  12. Hukumomin Senegal sun tsare shugabannin ɗalibai uku bayan rikici da ‘yan sanda

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Senegal sun ce sun tsare shugabannin ɗalibai uku sanannu bayan rikici mai tsanani da ya ɓarke tsakanin jami'an tsaro da dalibai masu zanga-zanga kan jinkirin biyan tallafin karatu a jami’ar Cheikh Anta Diop (UCAD) da ke Dakar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum ɗaya.

    A farkon makon nan, an kama ɗalibai 109 lokacin da rikicin ya ɓarke a jami’ar.

    Matakin Tsare shugabannin ɗaliban uku ya ƙara tsananta yanayin tashin hankali da aka shiga a jami’ar.

    Ƴan sanda sun ce ana zargin daliban da haddasa tashin hankali da shiga zanga-zangar da ba a sanar ba, da kuma lalata dukiyoyin gwamnati da na mutane masu zaman kansu.

    Rikicin tsakanin ɗalibai da jami’an tsaro ya yi sanadiyyar mutuwar wani ɗalibi me suna Abdoulaye Ba, wanda wasu rahotanni ke cewa ƴan sanda ne suka lakaɗa masa duka har sai da ya mutu, duk da cewa rahotanni sun sha bamban kan yadda lamarin ya auku.

    Gwamnati ta bayyana mutuwar ɗalibin a matsayin "abun baƙin ciki" kuma Firaminista Ousmane Sonko ya yi alƙawarin bincike mai zurfi kan lamarin a taron Majalisar Ministoci na ranar Laraba.

  13. Rasha na ƙoƙarin hana amfani da manhajar WhatsApp a ƙasar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Rasha ta yi yunƙurin toshe manhajar WhatsApp gaba ɗaya a ƙasar, in ji kamfanin manhajar yayin da gwamnatin kasar ke ci gaba da ƙara tsananta hana amfani da manhajojin tura saƙonni.

    Kamfanin WhatsApp mallakar Meta ya ce wannan mataki na nufin tilasta wa masu amfani da manhajar fiye da miliyan 100 a Rasha su koma amfani da wata manhajar lgamnatin kasar da za a iya saka wa ido.

    Mai magana da yawun Kremlin, Dmitry Peskov, ya ce Meta na iya ci gaba da aiki idan ta bi doka kuma ta shiga tattaunawa da gwamnati, amma ba za ta samu dama ba idan ta ƙi yin hakan.

    Hukumar kula da intanet ta Rasha, Roskomnadzor, ta sanar a farkon wannan mako cewa za ta ƙara takaita damar shiga manhajar Telegram saboda rashin tsaro.

    Telegram na da farin jini sosai a Rasha, musamman ma a tsakanin sojojin ƙasar a Ukraine.

    Rasha ta jaddada cewa WhatsApp da Telegram duk sun ƙi adana bayanan masu amfani na Rasha a cikin ƙasar, kamar yadda doka ta tanada.

    A cewar WhatsApp, kamfanin na yin duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa mutane sun ci gaba da amfani da manhajar a kasar duk da ƙuntatawar da ake samu.

  14. Jirgin ruwan yaƙin Turkiyya ya isa Somaliya don ingata tsaro

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani jirgin ruwan yaƙi ƙasar Turkiyya ya isa tashar jiragen ruwa ta Mogadishu jiya domin inganta tsaro a yayin da Ankara ke ƙara faɗaɗa kasancewar sojojinta a Somaliya.

    Rahotanni daga kamfanin dillancin labarai na ƙasar, Sonna, sun ce wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake hasashen shirin kafa sansanin sojojin ruwa a yankin Sanag na arewa maso gabashin Somaliya.

    Babban hafsan sojin Somaliya, Birgediya Janar Ibrahim Mohamed Mohamud, tare da ƙaramin ministan tsaro, Umar Ali Abdi ne suka tarɓi jirgin ruwan TCG Sancaktar.

    Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce ana sa ran ƙarin jiragen ruwan Turkiyya za su biyo baya nan gaba.

    Sonna ta bayyana cewa tura jiragen ruwan na cikin ƙoƙarin Somalia na ba fifiko ga ginawa da horaswa da kuma ƙarfafa rundunar ruwanta, tare da inganta tsaro a kan iyakokin ruwan ƙasar da hanyoyin zirga zirgar jiragen ruwa.

    Lamarin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan jiragen yaƙin saman Turkiyya ƙirar F-16 da aka tura Somalia ranar 29 ga Janairu suka yi shawagi a sararin samaniyar Mogadishu a ranar 3 ga Fabrairu.

    Somalia na ci gaba da ƙarfafa alaƙarta ta soja da tattalin arziƙi da diflomasiyya da ƙasashen Musulmi ciki har da Turkiyya da Saudiyya.

    Wannan na zuwa ne bayan Isra’ila ta amince da yankin Somaliland a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta a ranar 26 ga Disamba, lamarin da ya ƙara tsananta takaddamar diflomasiyya tsakanin Somalia da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

  15. KEDCO ya nuna damuwa kan matsalolin wutar lantarki a jihohin Arewa maso Yamma

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano, KEDCO, ya bayyana matukar damuwa kan matsalolin da ke shafar samar da wuta daga Kamfanin Wutar Lantarki na Najeriya da kuma kamfanin rarraba wutar ta ƙasa TCN zuwa jihohin Arewa maso Yamma.

    Kamfanin ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta umarci TCN da ya ba muhimmanci ga manyan ayyukan layin wutar lantarki da gyare gyare domin inganta isar da wuta a yankin.

    KEDCO ya ce "a halin yanzu hanyoyi biyu kacal ne ke kai wuta zuwa cibiyar Kano wato ta Kaduna da Jos kenan, lamarin da ya rage ƙarfin tsarin samar da wuta da kuma sa shi cikin hadarin katsewa idan matsala ta faru a daya daga cikin hanyoyin. "

    Ya ƙara da cewa akwai buƙatar ƙara tsaro da gyara da kuma faɗaɗa ƙarfin layin wutar Shiroro zuwa Mando har zuwa Kano domin rage yawan ɗaukewar wuta.

    Kamfanin ya ƙara da cewa a makonnin baya bayan nan ana yawan samun katsewar wuta a ƙarshen mako sakamakon ayyukan gyara da ake yi a layukan wuta, musamman aikin girka sabbin na’urorin OPGW.

    A cewarsa "wannan na matuƙar shafar harkokin masana’antu da rayuwar al’umma a jihohin yankin da kuma yankunan da yake aiki.

    Don rage tasirin matsalar, KEDCO ya ce yana aiki tare da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya da kuma Hukumar Tsarin Wutar Lantarki domin inganta daidaito a hidimar wuta.

    Ya kuma bayyana cewa tyna hanzarta shirye shiryen faɗaɗa samar da wuta a cikin gida domin rage dogaro gaba ɗaya ga cibiyar lantarki ta kasa.

  16. Mutum 15 sun mutu bayan kifewar kwale-kwale a kogin Nilu a arewacin Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Aƙalla mutum 15 ne suka mutu bayan wani kwale-kwale ya kife a kogin Nilu da ke arewacin Sudan.

    Ƙungiyar Likitocin Sudan ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis cewa lamarin ya faru ne da yammacin Laraba tsakanin Tayba Al-Khawad da Deim Al-Qarai a yankin Shendi, inda jirgin ke ɗauke da fasinjoji sama da 27 ciki har da mata da yara da kuma tsofaffi.

    Likitocin sun ce an gano gawawwaki akalla 15 zuwa yanzu, yayin da mutane shida suka tsira daga hatsarin.

    A halin yanzu mazauna yankin tare da masu aikin ceto na ci gaba da neman wasu da ake zaton sun ɓace a ruwa.

    Likitocin sun bayyana lamarin a matsayin wani mummunan bala’i na jin kai, suna cewa wannan hatsari ya sake nuna yadda sufuri ta ruwa ke da rauni da kuma rashin cika ka’idojin tsaro yadda ya kamata.

    Sun ƙara da cewa jinkirin zuwan masu ceto a farkon sa’o’i bayan kifewar jirgin ya ƙara tsananta girman asarar.

    Likitocin sun buƙaci hukumomi su gaggauta tura ƙwararrun jami’an ceto da kayan aikin bincike, tare da daukar matakan gaggawa domin inganta tsaron sufuri ta ruwa.

    Zuwa yanzu dai babu wata sanarwa daga hukumomin gwamnati kan lamarin.

  17. Kwankwasiyya ta mayar da martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta Kwankwaso

    ...

    Asalin hoton, Kano State Government/FB

    Ƙungiyar Kwankwasiyya a jihar Kano ta mayar da martani kan ƙudurin da wasu mambobin majalisar wakilan Amurka suka gabatar na a hukunta jagoranta Musa Kwankwaso dangane da zargin musguna wa Kiristoci a Najeriya.

    A cikin wata sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce "duk da cewa tana sane da muhimmancin damuwar ƙasashen duniya kan batutuwan haƙƙin dan'adam da ‘yancin addini, amma kuma Najeriya ta kasance ƙasa mai yalwar al’adu da addinai, kuma tana fuskantar matsalolin tsaro masu sarƙaƙiya da ke shafar kowane ɓangare ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba."

    A ranar Laraba ne wasu 'yan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da ƙuduri a zauren majalisar suna bukatar a sanya takunkumi kan Kwankwaso da wasu kungiyoyi da suka kira na "'yan bindiga'' wadanda suka zarga da taimakawa wajen cusguna wa mabiya addinin Kirista a kasar.

    Sai dai kungiyar ta Kwankwasiyya ta bayyana Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan kasa.

    Ta ce "yana da goyon bayan al’ummomin addinai daban daban, kuma a kullum yana inganta juriya da fahimtar juna tsakanin mabambantan ɓangarori."

  18. ’Yan Bangladesh na kaɗa ƙuri’a a zaɓen farko tun bayan hamɓarar da Sheikh Hasina

    ...

    Fiye da mutane miliyan 120 a fadin ƙasar Bangladesh ne ake sa ran za su kaɗa ƙuri’unsu domin zaɓen sabuwar gwamnati.

    Wannan ne karon farko da ake gudanar da zaɓe tun bayan zanga zangar matasa ta shekarar 2024 wadda ta kawo ƙarshen mulkin tsohuwar firaminista Sheikh Hasina.

    Zanga zangar da matasa suka jagoranta ta kawo ƙarshen shekaru 15 na mulkin Hasina, wanda masu suka suka ce ya kasance mai tsaurin ra’ayi.

    Mutane da dama na fatan cewa wannan zaɓe zai buɗe sabon shafi na shugabanci mai wakiltar ra’ayin jama’a a ƙasar.

    An buɗe rumfunan zaɓe tun da safe, kuma ana sa ran za a ci gaba da kaɗa ƙuri’a har zuwa ƙarfe 4:30 na yamma agogon ƙasar.

    Wannan ne karo na farko da ake gudanar da zaɓen ‘yan majalisa tare da kuri’ar raba gardama a lokaci guda.

    Ana sa ran sakamakon zaɓen zai fito gobe. Sheikh Hasina na ci gaba da zama a ƙasar Indiya tun bayan da aka hambarar da ita daga mulki sakamakon bore na ɗalibai a shekarar 2024.

  19. Abin da Bala Kaura ya ce kan rade-radin sauya shekarsa zuwa APC

    ...

    Asalin hoton, BSG

    Yayin da ake ci gaba da lissafa gwamnonin da suke sauya sheƙ zuwa jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad, ya ce yana nan a jamiyyarsa ta PDP daram.

    Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan jita-jitar da ake yaɗawa cewa yana shirin sauya sheka zuwa jam'iyyar APC.

    Gwamnan ya musanta hakan ne a wata hira da BBC ta yi da shugaban jam'iyyarsa ta PDP a jihar Bauchi wanda ya yi magana da yawun gwamnan.

    Pharmacist Sama'ila Adamu Burga, shugaban jam'iyyar PDP a jihar Bauchi, ya ce jita-jita ce kawai.

    "Da wa aka yi? kuma da wa gwamnan na Bauchi ya yi shawarar sauya shekar? to duk wannan jita-jitace kawai da soki burutsu," in ji shi.

  20. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.