Netanyahu ta tabbatar da bai wa ƴan bindigar da ke adawa da Hamas a Gaza makamai
Firaiministan Isra'ila Benjamen Netanyahu ya tabbatar gwamnatinsa na bai wa ƴan bindigar da ke adawa da Hamas a Gaza makamai.
Wata ƙabila da ta yi sansani a Rafah ta yi iƙirarin samar da tsaro ga jerin gwanon kayan agaji, amma aka zarge su da sata.
Da yake martani game da ikirarin cewar yana baiwa ƙungiyoyin masu laifi makamai, Mista Netanyahu ya ce ya yi amfani da abokan adawar Hamas wajen tserar da rayuwar sojin Isra'ila.
Wani ɗan siyasar adawa Yair Golan ya ce Mista Netanyahu ya zama barazana ga tsaron Isra'ila.

































