Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 19/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 19/01/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Haruna Kakangi

  1. Gwamnatin Kano za ta jagoranci ƙarar kisan mace da ƴayanta 6 a jihar

    Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta jagoranci shigar da ƙara kan kisan gillar da aka yi wa wata matar aure da ƴ aƴanta shida a unguwar Dorayi Chiranchi da ke birnin Kano, lamarin da ya jefa al’ummar jihar cikin alhini da girgiza.

    Gwamnatin ta bayyana kisan a matsayin mummunan aiki na rashin tausayi da rashin imani wanda ya girgiza zukatan al’ummar jihar tare da zama babban cin zarafi ga bil’adama da doka.

    A cikin wata sanarwa da babban lauyan jihar kuma kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude, SAN ya ce bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf, gwamnatin jihar ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan mamatan da daukacin al’ummar Kano.

    ''Gwamnati na tare da iyalan da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da cewa ba za a barsu su kaɗai ba a wannan mawuyacin lokaci," in ji sanarwar.

    Gwamnatin ta yaba wa rundunar ƴansandan jihar bisa gaggawar ɗaukar matakin bincike da ya kai ga kama manyan waɗanda ake zargi da aikata laifin.

    A cewar sanarwar, wannan mataki na nuna ƙudirin hukumomin tsaro na tunkarar aikata laifuka da dawo da amincewar jama’a ga tsaro da adalci.

    Gwamnatin ta jaddada cewa za a gudanar da shari'ar cikin gaggawa da ƙwarewa ta hannun Ofishin Babban Lauyan Jihar, inda za a kafa tawagar lauyoyi ta musamman domin tabbatar da adalci.

  2. Gobara ta laƙume shaguna a tsohuwar kasuwar Sokoto

    Wata gobara da ta tashi a safiyar Lahadi ta sanadiyyar wutar lantarki ta ƙone shaguna da dama a tsohuwar Kasuwar jihar Sokoto.

    Gobarar ta lalata kaya da dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

    Hukumar ba da agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) reshen Sakkwato ta ce tawagar gaggawarta ta garzaya wurin nan take bayan samun rahoton lamarin, tare da haɗin gwiwar Hukumar SEMA da Sashen Kashe Gobara.

    NEMA ta ce haɗin gwiwar hukumomin ya taimaka wajen shawo kan gobarar tare da hana ta yaɗuwa zuwa sauran sassan kasuwar.

    NEMA ta ce za ta ci gaba da fitar da ƙarin bayani game da lamarin yayin da ake samun sababbin bayanai.

  3. Mutum 39 sun mutu a hatsarin jirgin ƙasa a Sifaniya

    Akalla mutum 39 sun rasa ransu sannan wasu da dama sun jikkata bayan wasu jiragen ƙasa biyu sun yi taho mu gama da juna a kudancin Sifaniya.

    Ɗaya daga cikin jiragen na kan hanyarsa ne daga Malaga zuwa Madrid inda ya kauce wa hanyarsa, ya koma kan ɗaya layin dogon da a nan ne suka yi karo da wani jirgin da ke tafiya a kan layin dogon.

    Firaiministan Sifaniya, Pedro Sanchez ya bayyana lamarin a matsayin abin tashin hankali da kaɗuwa.

    Ministan harkokin sufuri na ƙasar ya ce har yanzu ba a san dalilin da ya sa jirgin ya kauce daga hanyarsa ba.

    Tuni dai masu aikin ceto suka ce kai wa ga waɗanda suka makale a cikin jirgin na wahala saboda yadda jiragen suka lotse.

  4. Waɗanne makamai Najeriya ke buƙata don yaƙi da ƴanbindiga?

    A makon da ya gabata ne Amurka ta sanar da kai wa Najeriya makaman yaƙi a wani wani mataki na taimaka wa ƙasar yaƙi da ƴanbindiga.

    Masu sharhi da ƴanƙasar da dama sun jima suna kokawa kan rashin wadatattun makamai ga jami'an tsaron ƙasar.

    A lokuta da dama an sha jin wasu jami'an tsaron ƙasar na ƙorafin rashin isassun makamai a matsayin ɗaya daga cikin matsalolin da suke fuskanta.

    Ƴanbindigar kan yi amfani da manyan makamai na zamani da ba kowane jami'in tsaro ke riƙewa ba.

    Hakan ya sa wasu ke ganin akwai buƙatar samar wa dakarun tsaron ƙasar wadatattun makamai na zamani domin daƙile ayyukan ƴanbindigar.

  5. China ta cimma burinta a fannin tattalin arziki a bara

    Tattalin arzikin ya haɓaka da kashi biyar cikin 100, kodayake yana cikin matakin da gwamnati ta yi hasashe.

    Sai dai tattalin arzikin ya nuna tafiyar hawainiya a bara, karon farko a tsawon gomman shekarun da aka jima ba.

    Matakin ya nuna raguwar da aka samu a kasuwanni cikin ƙasar.

    A makon daya gabata, Beijin ta rawaito cewa irin ribar da ta samu a wasu kayayyaki da ta siyar ko ta kai wasu ƙasashen duniya.

    To amma a cikin ƙasar ana ci gaba da samun faɗuwa musamman a ɓangaren cinikin gidaje.

  6. Lale maraba

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar Litinin, Mande tushen aiki ko da nasara na tsoronki, kamar yadda Hausawa ke yi mata kirari.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku kasance da mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa