Ƴanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 160 a coci a Kaduna

Asalin hoton, Getty Images
A jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, rahotanni sun nuna cewa wasu ƴanbindiga sun yi garkuwa da sama da mutane 160 a wasu coci-coci da ke ƙauyen Kurmin Wali a ƙaramar hukumar Kajuru a jihar.
Lamarin dai ya auku ne jiya Lahadi, lokacin da mutanen ke ibada a coci da ke ƙauyen.
Shi ma shugaban ƙungiyar kiristoci ta Najeriya CAN, reshen jihar Kaduna Reberan Joseph John Hayab ya tabbatar wa jaridar Daily Trust aukuwar lamarin.
Ya ce, "duk da cewa ban cika son ambata adadi ba, amma bayanan da na samu daga yankin na nuna cewa ƴanbindiga sun sace kusan mutum 172, amma guda 9 sun tsere sun koma gida, amma har yanzu ana neman mutum 163," in ji shi.
Ya ce ko ma dai mene ne maƙasudin sace mutanen, "ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba. Za mu ci gaba da ba jami'an tsaro da gwamnati haɗin kai domin tabbatar da ceto mutanen."
Har zuwa lokacin haɗa wannan labarin dai gwamnatin jihar Kaduna da rundunar ƴansandan jihar ba su ce komai ba.












