Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 25/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 25/11/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Isiyaku Muhammad da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Tanzania ta soke bikin ranar samun ƴancin kai

    Tanzania

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamnatin ƙasar Tanzaniya ta soke bikin ranar samun ƴancin kai na wata mai zuwa.

    Wata sanarwa da ta fito daga ofishin firaminista Mwigulu Nchemba ta ce za a ayi amfani da kuɗin da za a kashe a ranar bikin ne wajen sake gina ababen more rayuwa da suka lalace a tarzomar bayan zaɓen da aka yi a baya-bayan nan.

    Sanarwar dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan adawa da sauran ƙungiyoyi ke kira ga jama'a da su hallara a ranar bikin samun ƴancin kai - 9 ga watan Disamba - don gudanar da zanga-zanga game da kashe-kashen da aka yi bayan zaɓen shiugaban ƙasa a watan jiya.

    Ƴan adawa sun yi imanin cewa ɗaruruwan mutane ne suka mutu a wannan rikicin.

    Har yanzu dai gwamnati ba ta bayar da adadin waɗanda suka mutu ba, sannan ta kafa kwamitin bincike.

    Shugaba Samia Suluhu Hassan ta lashe zaɓen da kashi 98 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen wanda ƴan adawa suka bayyana a matsayin "izgili ga dimokraɗiyya".

    An dai haramtawa manyan abokan hamayyarta yin takara: Tundu Lissu na tsare ne bisa zargin cin amanar ƙasa, zargin da ya musanta, yayin da aka ƙi amincewa da takarar Luhaga Mpina.

    Tuni dai masu sa ido kan zaɓe masu zaman kansu suka bayar da rahoton alamun da ke nuna cewa an yi maguɗin zaɓe tare da cewa zaɓen bai cika ƙa'idojin dimokradiyya ba.

  2. 'Ƴanbindiga sun sace mutum 18 a jihar Kano'

    Gwamnan Kano

    Asalin hoton, Abba Kabir Yusuf/Facebook

    Ɗan majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar Tsanyawa da Ghari a jihar Kano, Injiniya Sani Bala Tsanyawa ya tabbatar da sace mutum 18 a wasu ƙayuka uku da ke yankin ƙaramar hukumar Tsanyawa.

    Hon. Tsanyawa ya shaida wa BBC cewa ƴanbindigar sun shiga ƙauyukan uku a cikin daren ranar Talata ɗauke da makamai inda suka yi garkuwa da mutanen ciki har da mata.

    Ya ƙara da cewa ƴanbingar na shiga ƙauyukan jihar ne daga jihar Katsina mai maƙwabtaka.

    ''Ƙauyukan da ƴanbindigar suka shiga sun haɗa da Biresawa, inda suka sace mutum biyar, sai ƙauyen Sundu da suka kama mutum huɗu, sai kuma ƙauyen Masaurari da suka kama mutum tara'', in ji ɗan majalisar.

    Ya ci gaba da cewa a wasu lokuta ƴanbindigar kan shiga ƙauyukan a kan babura, a wasu lokutan ma ya ce a ƙafa suke shiga ƙauyukan.

    A baya-bayan nan jihar Kano ta fara fuskantar hare-haren ƴanbindiga daga iyakarta da Katsina, wani abu da masana ke alaƙantawa da sulhu da ƴanbindiga da ake yi a wasu ƙananan hukumomin Katsina.

  3. 'Za a yi shekaru tare da kashe dala biliyan 70 kafin a sake gina Gaza'

    Gaza

    Asalin hoton, EPA

    Majalisar Dunkin Duniya ta yi kira ga kasashen duniya da su bayar da tallafa domin gina Gaza dake fuskantar kariyar tattalin arziki.

    Majalisar Dunkin Duniyar ta kuma ce Gabar Yamma da Kogin Jodan na fuksantar matsalolin tsaro da tattalin arziki irin su na farko a tarihi.

    Wani rahoto da Sashen Cinikayya da Raya Kasashe na Majalisar Dunkin Duniyar ya nunar da cewa tattalin arzikin Gaza ya fuskanci koma baya da kashi tamanin da uku cikin dari a sherar 2024 da ta gabata.

    Rahoton ya ce za a kwashe gomman shekaru tare da kashe dala biliyan saba'in kafin a sake gina yankin na Gaza da yaki ya daidaita.

  4. Ba a biya kuɗin fansa kafin sakin ɗaliban Kebbi ba - Gwamna

    Gwamnan Kebbi

    Asalin hoton, Nasir Idris/X

    Gwamnan Jihar Kebbi Nasir Idris ya ce ɗaliban jihar da aka kuɓutar daga hannun ƴanbindiga na cikin ƙoshin lafiya.

    A wani taron manema labarai da gwamnan ya gabatar a fadar gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi jim kaɗan bayan sanar da sakin ɗaliban, gwamnan ya gode wa shugaba Tinubu da sauran jami'an tsaro da suka taimaka wajen kuɓutar da ɗaliban.

    ''Daga bayanan da muke da su yanzu haka yaran suna kan hanya, kuma suna cikin ƙoshin lafiya, lafiyar kalau aka same su'', in ji shi.

    Gwamna Nasir Idris ya kuma ce ba a biya ko sisin kwabo ba a matsayin kuɗin fansa, domin karɓo ɗaliban 24.

    ''Mun bincika koda an biya kuɗin fansa ne, kuma daga bayanan da muka samu ba a biya kuɗin fansa ba, mu dai gwamnatin jihar Kebbi ba mu biya ko kwabo ba, kuma su ma jami'an da suke je karɓo su sun ce ba su je da kuɗi ba'', in ji shi.

    Gwamnan ya kuma gobe za a damƙa ɗaliban a hannun iyayensu.

    A makon da ya gabata ne aka sace ɗaliban a makarantar sakandiren ƴanmata da ke Maga a jihar.

  5. A gudanar da bincike kan hare-haren Isra'ila a Lebanon - MDD

    MDD

    Asalin hoton, EPA

    Hukumar kare hakkin danAdam ta Majalisar Duniyar ta yi kira da a gudanar da binciken gaggawa akan hare-haren da Isra'ila ta kai a Labanon kwanan nan, duk kuwa da cewa an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninta da Hezbollah.

    Hukumar ta bayar da misalai da hare-haren da aka kai a sansanin 'yan gudun hijira Falasdinawa da aka kai a makon jiya, da kuma ya yi sanadiyyar mutuwar mutum biyar da galibinsu kananan yara ne.

    Ma'katar lafiya ta Labanon ta ce fiye da mutum 330 ne aka kashe yayin da karin wasu 900 suka samu munanan raunuka a hare-haren da Isra'ila ta kai a cikin shekara daya.

    Isra'ila ta ce ta kai hare-haren ne domin karya lagon mayakan Hezbollah ta kuma zargi Iran da ke goyon bayansu da karya yarjejeniyar tsagaita wutar.

  6. Labarai da dumi-dumi, An kuɓutar da ɗaliban Kebbi 24 da ƴanbindiga suka sace a makon jiya

    Makarantar Maga

    Asalin hoton, Mustapha Ibrahim Maga/BBC

    Hukumomin Najeriya sun sanar da kuɓutar da ɗaliban Sakandiren ƴan mata da ke garin Maga a jihar Kebbi su 24.

    Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya wallafa a shafinsa na X, ya ce Tinubu ya yi wa ɗaliban maraba da dawowa.

    Shugaba Tinibu ya kuma ya yaba wa ƙoƙorin jami'an tsaron ƙasar kan kuɓutar da ɗaliban.

    Wani bidiyo da aka wallafa na yaran bayan kuɓutar da su, wanda BBC ta gani ya nuna yaran cikin wata motar bas tare da jami'an tsaro, suna bayyana sunayensu ɗaya-bayan ɗaya.

    Bidiyon ya kuma nuna yaran cikin murna da farin ciki yayin da suke tafiya a motar bas.

    Shugaban Najeriya ya kuma yi kira ga jami'an tsaron ƙasar su ƙara ƙaimi domin ku butar da ragowar ɗaliban Neja da suka rage a hannun ƴanbindiga.

    A makon da ya gabata ne wasu ƴanbindiga suka far wa makarantar tare da sace ɗalibai 25 da kashe malami guda.

    Bayanan da ke fitowa daga yankin na cewa ɗaliban an kan hanyar zuwa Birnin Kebbi, fadar gwamnatin jihar.

    Tun daga lokacin ne hukumomin ƙasar suka ɗauki matakai daban-daban domin kuɓutar da ɗaliban, daga ciki har da tura ƙaramin ministan tsaron ƙasar, Mohammed Bello Matawalle zuwa Kebbi domin ya kula da ƙoƙarin gwamnati na kuɓutar da ɗaliban.

  7. Tinubu ya buƙaci sojoji su killace dazukan Kwara, Kebbi da Neja

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci, jami'an tsaron ƙasar su killace dazukan jihohin Kwara da Kebbi da kuma Neja, inda a baya-bayan nan ake samun ƙaruwar hare-hare tare da garkuwa da mutane.

    Cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban ƙasar kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Daare ya wallafa a shafinsa na X, ya ce Tinubu ya buƙaci runsunar sojin saman ƙasar ta faɗaɗa sanya idanu ta sama kan dazukan, waɗanda ya yi imanin cewa nan ne mafakar yanbindigar.

    Shugaba Tinubu ya buƙaci sojojin saman su faɗaɗa tsaron dazukan domin taimaka wa dakarun ƙasa.

    A baya-bayan nan ne dai an samu garkuwa da ɗaliban a jihohin Kebbi da Neja da masu ibada a jihar Kwara

  8. Venezuela ta buƙaci kamfanonin jiragen sama su dawo da zirga-zirga a ƙasar

    ...

    Asalin hoton, MIGUEL GUTIERREZ/EPA/Shutterstock

    Venezuela ta shaidawa wa kamfanonin jiragen sama na ƙasa da ƙasa da su dawo da zirga-zirgar jiragen sama zuwa ƙasar cikin sa'o'i 48 ko kuma a soke masu lasisin aiki a ƙasar gaba ɗaya.

    Kamfanonin jiragen sama da dama sun dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa Venezuela bayan da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Amurka ta yi gargadin cewa za ta "ƙara yawan ayyukan soji" a yankin.

    Gargadin ya zo ne a daidai lokacin da Amurka ta matsa lamba kan gwamnatin Venezuela, inda ta aike da jirgin ruwan yaƙi mafi girma a duniya zuwa yankin kudancin Caribbeai.

    Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta ƙasa da ƙasa (IATA) ta gargadi hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Venezuela cewa soke izinin jiragen sama zai mayar da ƙasar saniyar ware.

    Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Venezuela (Inac), wadda ke ƙarƙashin ma’aikatar sufuri ta ƙasar, ta ba da wannan wa’adin ne a ranar Litinin.

    Daga cikin kamfanonin jiragen da abin ya shafa sun haɗa da Iberia na Sifaniya da Air Europa da Plus Ultra da Gol na Brazil da Latam na Chile da Avianca na Colombia da TAP na Portugal da kuma Turkish Airlines.

  9. Red Cross ta karɓi gawar wanda aka yi garkuwa da shi a Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Palestinian Islamic Jihad (PIJ) da Hamas sun miƙa wa ƙungiyar agaji ta Red Cross wani akwatin gawa wanda ƙungiyoyin suka ce yana ɗauke da gawar ɗaya daga cikin mutane uku da suka mutu a Gaza, a cewar sojojin Isra'ila.

    Za a miƙa gawar ga sojojin Isra'ila, waɗanda za su kai su cibiyar nazarin magunguna ta Isra'ila da ke Tel Aviv don tantancewa.

    Tun da farko, PIJ da Hamas sun sanar da cewa an gano gawar wani ɗan Isra'ila da aka yi garkuwa da shi a tsakiyar Gaza a ranar Litinin.

    Ofishin Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi gargaɗin cewa yana kallon "da tsananin jinkirin miƙa gawarwakin cikin gaggawa", yana mai cewa hakan ya zama karya sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta na Gaza da aka shafe makonni shida ana yi.

    A ƙarkashin zangon farko na yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka shiga tsakani, wadda ta fara aiki a ranar 10 ga watan Oktoba, Hamas ta amince da mayar da mutanen Isra'ila 20 da suka yi garkuwa da su da gawarwakin mamatan Isra'ila da na ƙasashen waje 28 da har yanzu suke a Gaza cikin sa'o'i 72.

    An saki dukkan waɗanda aka yi garkuwa da su da su ke raye a ranar 13 ga watan Oktoba domin musayarsu da fursunonin Falasdinawa 250 da ke Isra'ila da kuma fursunoni 1,718 da a ke riƙe da su a Gaza. Ya zuwa yanzu, an miƙa gawarwakin mamatan Isra'ilawa 22 da aka yi garkuwa da su, tare da wasu ƴan ƙasashen waje uku.

  10. RSF da gwamnatin Sudan sun yi watsi da tayin Trump na tsagaita yaƙi - Amurka

    Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban mai ba Shugaban Amurka Donald Trump shawara akan Afirka ya ce dakarun sojin Sudan da na 'yan tawayen RSF sun yi watsi da tayin da Amurka ta yi musu na neman a tsagaita wuta.

    Massad Boulos ya ce ya ce ya saurari bangarorin biyu bayan da aka bayar da sanarwar tsagaita wutar a jiya Litinin tare da cewa ya zama wajibi su kawo karshen yakin basasar da ya dauki lokaci ana yi ba tare da gindaya kowane sharadi ba na dole ba.

    Rundunar sojin Sudan din ta yi watsi da wani daftarin dakatar da buɗe wutar da ke samun goyon bayan asasr Hadaddiyar Daular Larabawa, tana mai cewa yarjejeniyar ta fifita RSF.

    Yarjeniyoyin dakatar da buɗe wuta da aka rika yi a baya - sun rika rushewa, tun ba a je ko'ina ba. Dubban fararen hula aka kashe tun da yaƙin basasar ya ɓarke a 2023.

  11. Muna fata Ukraine za ta amince da daftarin tsagaita yaƙi - Amurka

    Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'an gwamnatin Amurka sun ce akwai kyakkyawan fatan Ukraine za ta amince ta sanya hannu akan daftarin yarjejeniyar tsagaita wuta.

    Tawagar ta Amurka a birnin Abu Dhabi na ci gaba da tuntubar sassan biyu a wani matakin dunke barakar da ke tsakaninsu.

    Wakilin BBC ya ce: "A yanzu daftarin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta da aka gabatar wa Ukraine na dauke da sauye-sauye da ba su kunshi wasu bukatun Rasha ba."

    Hakan na zuwa ne yayin da a lokaci guda kasashen Rasha da Ukraine suka shafe daren jiya suna yi wa juna luguden wuta.

  12. Gidauniya ta ɗauki nauyin tiyatar ido ta mutum 2000 a Kaduna

    Ido

    Asalin hoton, Yahya Rayya Jingle

    Wata gidauniya ta ɗauki nauyin yi wa sama da mutum 2000 tiyatar ido kyauta tare da duba wasu mutanen a ba su magani a jihar Kaduna.

    Gidauniya ta Fatima Tajuddeen Abbas ta ɗauki nauyin ne a garin Zaria da ke ƙaramar hukumar ta Zaria a jihar Kaduna, inda aka duba mutane masu fama da na'ukan ciwon ido da suka haɗa da yanar ido da sauransu.

    Da yake jawabi wajen ƙaddamar da aikin, shugaban kula da aikin, Barista Aminu Ramalan ya ce gidauniyar ta ɗauki nauyin gudanar da aikin ne a ƙarƙashin tallafin Hajiya Fatima Tajuddeen Abbas, matar shugaban majalisar wakilan Najeriya.

    A nasa jawabin, shugban ƙaramar hukumar Zaria, Jamil Ahmad Muhammad ya ce ana aikin ne a matsayin tallafi ga mutane marasa ƙarfi, sannan ya yaba da ƙoƙarin gidaunar wajen taimakon marasa galihu.

    Jagoran likitocin da suke tiyatar, Dr Kamilu Saleh suna aikin ne tare da wasu ƙwararrun likitoci daga ƙasar Turkiyya.

    Wata wadda ta amfana da shirin, Fatima Umar ta ce tana godiya ga gidauniyar, inda ta ce, "Na yi shekaru ina fama da ciwon ido, amma yau cikin ikon Allah gidauniyar nan ta ɗauki nauyin dubani kyauta,"

    Shi ma wani dattijo mai suna mallam Ibrahim Ali ya ce rashin kuɗi ya sa ya daɗe yana fama da matsalar ta ido kafin gidauniyar ta ɗauki nauyin yi masa aiki.

  13. MDD ta yi Allah-wadai da garkuwa da ɗaruruwan mutane a Najeriya

    Ƴanbindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Allah-wadai da hare-hare da garkuwa da mutane da ta ce ya koma ɗanye a arewa ta tsakiyar Najeriya, inda ta yi kira ga hukumomin ƙasar da su ɗauki matakin gaggawa domin daƙile hare-haren tare da tabbatar da hukunci kan masu aika-aikar.

    "Mun yi mamakin yadda hare-haren suka dawo a arewa ta tsakiyar Najeriya," kamar yadda kakakin majalisar, Thameen Al-Kheetan ya bayyana wa manema labarai a birnin Geneva.

    "Muna kira ga hukumomin Najeriya a dukkan matakai da su ɗauki gaggawa domin kiyaye ci gaba da aukuwar irin waɗannan hare-haren, sannan ta tabbatar ta hukunta masu aika-aikar nan."

    Ya ce, "an sace aƙalla mutum 402, yawancinsu ɗaliban makaranta a jihohin Neja da Kebbi da Kwara da Borno daga ranar 17 ga Nuwamba. Amma a cikinsu guda 88 kawai aka iya kuɓutarwa," in ji shi.

    A ƙarshe ya yi kira ga gwamnatin Najeriya ta yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa ta kuɓutar da ɗaliban da sauran mutanen da suke hannun ƴanbinddiga.

  14. An tsaurara tsaro a makarantun jihar Legas

    Ƴansanda

    Asalin hoton, Getty Images

    An tsaurara tsaro a garuruwan cikin jihar Legas biyo bayan ƙaruwar hare-hare da garkuwa da mutane da aka fuskanta a wasu makarantu a arewacin Najeriya.

    Tuni ƴansandan suka ƙara yawan motocin sintiri a makarantu da wuraren ibada da sauran kadarorin gwamnati da ke jihar, wadda cibiya ce ta kasuwanci.

    Wannan matakin na zuwa ne bayan an yi garkuwa da ɗaruruwan mutane, yawanci ƴan makaranta a wasu hare-hare daban-daban da aka yi a cikin mako biyu da suka gabata a Najeriya.

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ɗan jihar Legas ne, jihar da ya mulka na tsawon wa'adi biyu, sannan ya yi sanata kafin ya zama shugaban ƙasa.

  15. Sufeton ƴan sandan Najeriya ya isa jihar Kebbi inda aka sace ɗalibai sama da 20

    sufeton ƴan sanda da gwamnan Kebbi

    Asalin hoton, NIGERIA POLICE FORCE

    Babban sufeton ƴan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya isa jihar Kebbi, bayan ƴan bindiga sun sace dalibai da dama a jihar makon da ya gabata.

    Bayan isar sa, sufeton ƴan sandan ya kai ziyara fadar gwamnatin jihar inda ya ke ganawa da gwamnan jihar Dakta Nasiru Idris.

    Ziyarar ta sa na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da aikin ceto ɗalibai ƴan mata 23 da aka sace a makarantar kwana ta Maga da ke karamar hukumar Danko/Wasagu a makon da ya gabata.

    A ranar Lahadin da ta gabata, Egbetokun ya yi wata ganawa da shugaban Najeriya Bola Tinubu a fadar gwamnatin ƙasar kan yadda matsalar tsaro ke ƙara taɓarɓarewa, musamman hare haren baya bayan nan a jihohin Kebbi da Neja da Kwara.

  16. An dakatar da tashin jirage a India saboda tokar aman dutse a Habasha

    hoto daga sararin samaniya

    Asalin hoton, Reuters

    An dakatar da tashi da saukar wasu jirage a India sakamakon yadda tokar da ta fito daga wani dutse da ya yi aman wuta a Habasha ya turnuke sararin samaniyar ƙasar.

    Wasu jiragen kuma an jinkirta tashinsu, yayin da wasu kuma suka sauya hanya, a yayin da tokar dutsen Hayli Gubbi, ya soma bazuwa a tekun Maliya.

    Dutsen ya yi aman wuta ne a ranar Lahadi, karo na farko cikin kusan shekaru dubu goma, wanda ya fitar da hayaƙin da ya yi tsawon kilomita 14 zuwa sararin samaniya.

    Hukumar kula da jiragen sama na Indiya ta gargaɗi masu tuƙa jiragen su guji bi ta yankunan da ke kusa da tokar, su kuma bayar da rahoton duk wani abu da ya faru wanda ba a saba gani ba musamman a injinan jiragensu.

  17. Ƴanbindiga sun sake sace mutum 11 a Kwara

    ƴan bindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun bayyana cewa ƴanbindiga sun sake kai hari, inda suka sace aƙalla mutum 11 a garin Isapa da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara.

    Rahotannin sun bayyana cewa ƴanbindigar sun kai harin ne a yammacin ranar Litinin, a garin da ke kusa da garin Eruku inda aka sace wasu masu ibada kwanakin baya.

    A cewar wata jarida mai zaman kanta DailyTrust, mazaunin garin ya tabbatar mata cewa ƴanbindigar da suka kai aƙalla 30 ne suka shiga garin suna harbe-harbe har suka tarwatsa mutane.

    Rahotannin sun kuma ce ƴanbindigar sun yi awon-gaba da aƙalla mutum 11, ciki har da ƙananan yara, da mai juna biyu, kuma huɗu daga cikinsu ƴan gida ɗaya ne.

    Kwamishinan ƴansandan jihar, Adekimi Ojo ya tabbatar wa jaridar da faruwar lamarin, sai dai ya ce ba shi da cikakken bayani, amma yana kan hanyarsa zuwa garin, inda ya ce daga bisani zai yi ƙarin haske.

    Wannan sabon harin na zuwa ne kwana guda bayan da aka sanar da kuɓutar da wasu mutane sama da 30 da aka sace a wani coci a jihar a makon da ya gabata.

    Matsalar tsaro da sace mutane dai na ci gaba da ƙaruwa a Najeriya, musamman a arewacin ƙasar, inda a yanzu haka ake ci gaba da neman wasu ɗalibai da aka sace a makon da ya gabata.

  18. Mata a Nijar sun koka kan yadda ake nuna musu wariya a alamuran ci gaba

    Matasa mata a jamhuriyar Nijar na nuna damuwa kan yadda suka ce ana nuna masu wariya wajen bayar da guraben aiki da kuma abin da ya shafi sauran harkokin rayuwa.

    Sun bayyana hakan ne a yayin wani taro da aka yi da ya haɗa shugabannin matasa maza da mata daga ƙasashen Sahel da suka hada da Nijar, da Mali da Burkina Faso, da kuma Senegal da sauransu.

    Adama Garba da ta wakilci Nijar a taron da aka yi a Yamai, ta ce babban kalubale da mata a Afirka ke fuskanta shi ne rashin bai wa abin da suke faɗa muhimmanci, musamman a Afirka ta Yamma.

    Ta ce akwai bukatar basu damar faɗin albarkacin bakinsu, da kuma faɗin abin da ya kamata a yi wa mata.

    Adama ta kuma ce gyara makomar ƙasa ba abu ne da za a yi da bangare guda ba, a cewar ta, tafiya ce ta haɗin gwiwa.

    Ta koka kan cewa a lokuta da dama idan za a yi taruka ba a gayyatar yawan matan da ya dace, kuma kaɗan ɗin da aka gayyata ma ba a sauraren su.

    ' Afrika ta gobe sai anyi da mata da matasa, muna da gudunmawar da za mu bayar a fannin tattalin arziki da tsaro da kowane fanni' in ji ta.

  19. Ba a ɗaukar matakan da suka kamata kan ɗaliban da aka sace - Bishop Yohanna

    allon makarantar St Mary

    Asalin hoton, BBC VIA ZAHARADEEN

    Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen jihar Neja, Bishop Bulus Dauwa Yohanna ya ce zuwa yanzu hukumomi ba su ɗauki wani 'matakin a zo a gani' ba kan batun ceto yaran da aka sace.

    Bishop Yohanna, wanda shi ne kuma mai makarantar da aka sace ɗaliban, ya shaidawa BBC cewa matakin kawai da aka ɗauka zuwa yanzu a hukumance shi ne tattara sunayen yaran da ƴan bindigar suka yi awon gaba da su.

    Ya kuma musanta batun cewa sun ƙi bin umurnin da gwamnati ta bayar na rufe makaranatar saboda barazanar tsaro, a cewar sa babu wani bayani da suka samu dangane da hakan.

    A ranar juma'ar da ta gabata ne ƴan bindiga suka far wa makarantar Katolika ta St Mary da ke garin Papiri a ƙaramar hukumar Agwara da ke jihar Neja, inda suka sace ɗalibai da malamai sama da 300.

    Sai dai makarantar ta ce 50 daga cikin ɗaliban sun yi nasarar kuɓuta.

    Iyayen yaran sun shaida wa BBC cewa yaran ƴan shekara 6 ne zuwa 18.

  20. Akwai fargabar mutum miliyan 35 a arewacin Najeriya za su yi fama da yunwa a 2026 - MDD

    yaro riƙe da roba

    Asalin hoton, Getty Images

    Shirin Abinci na Majalisar ɗinkin duniya, WFP, ya yi gargadin cewa akwai fargabar aƙalla mutum miliyan talatin da biyar da ke arewacin Najeriya za su fuskanci rashin abinci mai tsanani a shekara mai zuwa saboda ƙaruwar hare-hare da taɓarɓarewar tsaro.

    Wani mai magana da yawun WFP ya ce alummomi da dama na fama da matsaloli sakamakon karuwar hare haren ƴan bindiga, da yanayin tattalin arzikin ƙasar wanda ke nuna ƙaruwar buƙatar tallafi.

    Shirin samar da abincin dai ya ja baya da ayyukansa na samar da abinci mai gina jiki a baya bayan nan a arewa maso gabashin Najeriya, kuma abincin da ya ke bayarwa na tallafi zai ƙare nan da watan Disamba.