Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Shugaba Buhari zai tafi Masar
Shugabn Najeriya Muhammadu Buhari zai tafi garin Aswan na kasar Masar ranar Talata domin halartar wani taron zaman lafiya da ci gaba a nahiyar Afirka.
Kamar yadda fadarsa ta bayyana a shafinta na Twitter, shugaban zai shafe ranakun Alhamis da Juma'a yayin taron.
Ta kara da cewa taron, wanda aka kira shi da suna "An Agenda for Sustainable Peace and Development in Africa", wani yunkuri ne da nahiyar Afirka take yi na nemo wa kanta hanyoyin shawo kan matsalolin tsaro da kuma cigaba.
Wannan ne balaguro na 12 zuwa wajen Najeriya da Buhari zai yi tun bayan cin zabensa a karo na biyu.
Tafiye-tafiyen Buhari bayan cin zabe:
30- 2 Yuni - Saudiyya - Taron kungiyar kasashen musulmai
6-2 Yamai - Taron Tarayyar Turai kan kasuwancin bai daya
26 Yuli -Liberia - Bikin samun 'yancin kai
25-30 -Japan - Taro kan alakar Tokyo da Afirka
14 Satumba - Burkina Faso - Taron ECOWAS kan ta'addanci
25 Satumba - 1 Oktoba - New York City - US - Ziyarar aiki.
2-3 Oktoba - Pretoria - Afirka ta Kudu - Ziyarar aiki
21-23 Oktoba - Sochi - Rasha
28 - 31 Oktoba - Riyadh - Saudiyya - Taron kasuwanci
31 - 17 Nuwamba - London - Burtaniya - Ziyara don kai
28 - 29 Nuwamba - Malabo, Equatorial Guinea - ziyarar aiki