Indiya: Rumfa ta fado kan masu bauta ta kashe mutum 14

Bayanan bidiyo, Yadda mutane suka taru a wajen da lamarin ya faru
Lokacin karatu: Minti 1

A kalla mutum 14 ne suka mutu yayin da wasu 50 suka jikkata lokacin da ruwan sama da iska mai karfi suka jawo wata babbar rumfa ta fado a jihar Rajasthan ranar Lahadi.

Kamfanin dillacin labarai na Reuters ya ruwaito cewa wasu da dama sun mutu ne sakamakon jan su da wutar lantarki ta yi a yayin da rumfar ta kifa a kansu, wasu kuma sun mutu ne sakamakon fado musu da baraguzai ya yi.

Kusan mutum 300 ne suke wajen bautar a lokacin da abin ya faru, a cewar jaridar Hindustan Times.

Lamarin ya auku ne a gundumar Barmer da ke arewa maso yammacin jihar.

Indian injured people are being treated at a hospital in Barmer

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, An kai wadanda suka jikkata asibitin garin Barmer

Minsitan agajin gaggawa na jihar Bhanwar Lal Meghwal, ya tuhumi masu shirya ibadar dalilin da ya sa ba su kashe wutar lantarki ba ganin yadda ake mamakon ruwan saman.

Tuni dai aka kaddamar da bincike kan lamarin.

Firaministan Indiya Narendra Modi ya ce lamarin abu ne mara dadi, a wani sako da ya wallafa a shafin Twitter a ranar Lahadi, inda ya mika sakon ta'aziyyarsa ga iyalan wadanda suka mutu.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Presentational white space
map