Ramadan 2019: Musulmi sun fara azumi

Asalin hoton, Getty Images
A Najeriya, mai alfarma sarkin Musulmi, Sultan Sa'ad Abubakar III, wanda shi ne shugaban majalisar koli kan harkokin addinin musulunci ya bayyana ganin watan a garuruwa daban-daban a Najeriya a wani taron manema labarai da aka gudanar a daren Lahadi.
Wannan na zuwa ne bayan ganin jinjirin watan da aka yi a wurare daban-daban a fadin duniya.
Kwamitin ganin wata na Najeriya ya wallafa jawabin sarkin a shafin Twitter inda sarkin ya umarci jama'a da su tashi da azumi ranar Litinin.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Akasarin Musulmai a fadin duniya za su tashi da Azumin watan Ramadan ranar shida ga watan Mayun 2019 wanda hakan ya zo dai-dai da daya ga watan Ramadan 1440.
Sarkin ya yi kira da a yawaita ibada a cikin watan na Ramadan kuma a ci gaba da addu'a ga shugabanni.
Baya ga Najeriya Musulmai a wasu kasashen duniya irin su Saudiyya za su fara azumin na watan Ramadana a ranar Litinin.
Ramadan dai wata ne mai alfarma ga musulmi inda ake matsa kaimi kan ibada da addu'o'i.







