Trump ya soki yadda ake ba da rahoton yaƙin Amurka da Iran

Asalin hoton, Reuters
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi kakkausar suka kan yadda kafafen yaɗa labarai ke bayar da rahotannin da suka shafi yaƙin Amurka da Iran, inda ya bayyana rahoton da ke cewa Iran na da ƙarfin soji a matsayin "cin amanar ƙasa".
Saƙon da ya wallafa a shafinsa na dandalin Truth social ya zo ne sakamakon rahoton da jaridar New York Times ta wallafa cewa har yanzu Iran tana riƙe da kashi biyu bisa uku na makamanta masu linzami, kuma ta sake samun damar yin amfani da yawancin cibiyoyinta na ƙarƙashin ƙasa.
Jaridar ta ce rahotannin da gwamnatin Trump ke fitarwa da ke nuna ta ɗaiɗaita sojojin Iran ya yi hannun riga da abin da hukumomin leƙen asirin Amurkan ke fada a bayan fage.

