Buhari zai yi hutun kwana 10 a Landan

Buhari

Asalin hoton, Getty Images

Lokacin karatu: Minti 1

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai fara hutun kwana 10 a ranar Juma'a, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu, ya wallafa, a shafinsa na Twitter, ya ce, shugaban ya rubuta wa Majalisar Dokokin kasar takardar sanar da ita hakan.

Kauce wa X, 1
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 1

Ya ce shugaban zai yi hutun ne a birnin Landan a kasar Birtaniya. Amma sanarwar ba ta yi magana kan ko shugaban zai ga likitocinsa kamar yadda ya saba idan ya je kasar ba.

Har ila yau ya ce Mataimakin Shugaban Kasar Yemi Osinbajo ne zai jagoranci kasar a matsayin mukaddashin shugaban kasa a lokacin hutun.

Sai dai ba wannan ne karon farko da shugaban ya dauki hutu ba, don ko a farkon shekarar 2017 ya yi hakan.

Kauce wa X, 2
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 2