Kotu ta wanke tsohon Gwamnan jihar Sakkwato Attahiru Bafarawa

Asalin hoton, Twitter/EFFC
Wata babbar kotu a jihar Sakkwato ta wanke tsohon Gwamnan jihar Attahiru Bafarawa daga tuhumar karkata kudi da karbar kudin sata da sauransu.
Mai shari'a Bello Abbas ya wanke dan siyarar tare da wadansu mutane hudu daga dukkan tuhume-tuhume da Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati a Najeriya (EFCC) take musu.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Hukumar ta wallafa labarin wanke dan siyasar ne a shafinta na Twitter a ranar Talata.
Alkalin kotun ya ce mai gabatar da kara bai nuna kwararan shaidu da suke tabbatar da tuhume-tuhumen da ake musu ba.
"Babu kwararan hujjoji da za su tabbatar da cewa mutanen sun aikata laifukan da ake tuhumarsu," in ji shi.
Sai dai hukumar EFCC ta ce ba ta gamsu da hukuncin ba, kuma za ta daukaka kara, kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
An dai fara sauraren wannan shari'ar ce a watan Disambar shekarar 2009.







