Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Gwamnan tsohuwar Jihar Kaduna Lawal Kaita ya rasu
Gwamnan tsohuwar Jihar Kaduna Alhaji Lawal Kaita ya rasu bayan fama da rashin lafiya.
Rahotanni sun ce fitaccen dan siyasar a Najeriya, ya rasu ne a yau Talata a wata asibiti a birnin Tarayya Abuja.
Tsohon gwamnan ya rasu yana da shekaru tamanin da biyar a duniya.
Kaita ya yi gwamna ne a inuwar jam'iyar NPN a tsohuwar jihar Kaduna a 1983 kafin sojoji su yi wa Shagari juyin mulki.