Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Ku San Malamanku tare da Malam Abdurrahman Ibrahim Idris
Ku San Malamanku tare da Malam Abdurrahman Ibrahim Idris
Abdurrahman Ibrahim Idris malamin addinin Musulunci ne da aka haifa a garin Bauchi da ke arewacin Najeriya a shekarar 1982.
Ya yi karatun firamare da sakandare a garin na Bauchi, kafin ya yi digirinsa na farko a Jami'ar Maiduguri, da kuma na biyu a ƙasar Sudan.
Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, malam Abdurrahman na yin digirin digirgir Jami'ar Musulunci ta Uganda.
Ya yi karatun soro a hannun malamai da dama, ciki har da mahaifinsa Imam Ibrahim Idris, da malam Aliyu Yakubu, da Dr Ja'afar Danbaba.