Ku San Malamanku tare da Malam Abdurrahman Ibrahim Idris
Ku San Malamanku tare da Malam Abdurrahman Ibrahim Idris
Abdurrahman Ibrahim Idris malamin addinin Musulunci ne da aka haifa a garin Bauchi da ke arewacin Najeriya a shekarar 1982.
Ya yi karatun firamare da sakandare a garin na Bauchi, kafin ya yi digirinsa na farko a Jami'ar Maiduguri, da kuma na biyu a ƙasar Sudan.
Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, malam Abdurrahman na yin digirin digirgir Jami'ar Musulunci ta Uganda.
Ya yi karatun soro a hannun malamai da dama, ciki har da mahaifinsa Imam Ibrahim Idris, da malam Aliyu Yakubu, da Dr Ja'afar Danbaba.



