Tambayoyin da har yanzu ba a san amsarsu ba game da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Yara Falasdinawa a Gaza da wasu mace da namiji a birnin Tel Aviv dauke da farin ciki a fuskokinsu lokacin da aka sanar da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Asalin hoton, Anadolu / Getty Images

Bayanan hoto, Yadda mutane suka yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza daga dukkanin ɓangarori biyu
Lokacin karatu: Minti 6

Isra'ila da Hamas sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bayan shafe wata 15 ana gwabza faɗa a Gaza.

Firaiministan Qatar, Sheikh Mohammed bin Abdul Rahman Al Thani ya ce yarjejeniyar za ta fara aiki ne a ranar L;ahadi, matuƙar ta samu amincewar majalisar zartaswar Isra'ila.

An cimma wannan matsaya ce bayan watanni da dama da aka kwashe ana tattaunawa sanadiyyar rashin yarda da juna tsakanin Hamas da Isra'ila.

Wata yarinya Bafalasɗiniya na duba gidansu da wani harin Isra'ila ya lalata a sansanin ƴan gudun hijira na Al Maghazi, a tsakiyar Zirin Gaza a ranar 3 ga watan Janairu 2025

Asalin hoton, Mohammed Saber / EPA

Bayanan hoto, Wata yarinya Bafalasɗiniya na duba gidansu da wani harin Isra'ila ya lalata a sansanin ƴan gudun hijira na Al Maghazi, a tsakiyar Zirin Gaza a ranar 3 ga watan Janairu 2025

Tun farko Hamas ta buƙaci dole a kawo ƙarshen yaƙin kafin ta saki ƴan Isra'ila da take garkuwa da su, sai dai Isra'ila ba za ta amince da hakan ba.

Yarjejeniyar ta ƙunshi batun tsagaita wuta, yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan sauran batutuwa.

Sai dai abin da babu tabbas shi ne ko hakan zai kawo ƙarshen yaƙin, domin kowa ya huta.

Ɗaya daga cikin alwashin da Isra'ila ta sha game da yaƙin shi ne lalata ƙarfin soji da na jagorancin ƙungiyar Hamas.

Duk da cewa Isra'ila ta yi wa Hamas gagarumar illa, har yanzu Hamas na da sauran ƙarfin sake curewa da ci gaba da ayyukanta.

Sakin waɗanda ake garkuwa da su da kuma fursunoni

Iyalan wadanda Hamas ta yi garkuwa da su a Gaza, da masu goyon bayansu daukie da hotunan mutanen a wajen shalkwatar jam'iyyar Likud, ranar 8 ga watan Junairun 2025, a lokacin zanga-zangar kiran a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da kubutar da 'yan uwansu

Asalin hoton, EPA

Bayanan hoto, Isra'ila na son Hamas ta mayar mata da mutanen da take garkuwa da su a matsayin ɗaya daga cikin ƙa'idojin yarjejeniya

Babu tabbas kan yawan sauran waɗanda ake garkuwa da su da suke raye a yanzu, da kuma waɗanda suka mutu, haka nan babu tabbas ko Hamas na da masaniya kan inda sauran mutanen da ba a san halin da suke ciki ba suke.

A ɗaya ɓangaren, akwai wasu fursunoni da Hamas ta buƙaci Isra'ila ta saki amma Isra'ilar ta ce ba za ta sake su ba.

An haƙiƙance cewa mutanen da Isra'ila ta ce ba za ta saki ba su ne waɗanda ke da hannu a harin da ƙungiyar ta kai na ranar 7 ga watan Oktoba.

Haka nan babu tabbas ko Isra'ila za ta amince ta janye daga wurare masu muhimmanci wurin hana kai mata hari da ta jibge dakarunta, a lokacin da aka ayyana.

Wani yaro na tura keken guragu, dauke da jarkar ruwa akai a sansanin 'yan gudun hijira da ke Khan a kudancin zirin Gaza, ana iya ganin yadda gidaje suka ruguje babu sauran mamora

Asalin hoton, Bashar Taleb / AFP / Getty Images

Bayanan hoto, Yaro a Gaza

Yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin biyu ba ta da tabbas.

Yarjeniyoyin tsagaita wuta da aka cimma tsakanin Isra'ila da Hamas a baya sun samu cikas sanadiyyar rikice-rikice, waɗanda daga baya kan wargaje.

Sarƙaƙiya da kuma lokutan da aka tsara na aiwatar da wannan yarjejeniya na nuna cewa duk wani rashin jituwa, komai ƙanƙantarsa zai iya zama barazana ga zaman lafiyar.

Matan Falasdinu tsye a jikin tagar wani gini da ba a kammala ba da kuma ya daidaice, gabannin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas a ranar 15 ga watan Junairu 2025.

Asalin hoton, Mahmoud Issa / Reuters

Ko Trump zai iya samun yabo kan yarjejeniyar?

Zababben shugaban Amurka Donald Trump, ya na dagawa mutane hannu a lokacin da ya kai ziyara wurin taro na Horizon a Clive, Iowa, U.S. Ranar 15 Junairu 2024.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Zababben shugaban Amurka, Donald Trump

Shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump ya yi iƙirarin cin nasara kan yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas. A cewarsa, ''cimma yarjejeniyar tsagaita wutar mai muhimmanci ya faru ne sakamakon nasarar da muka yi mai cike da tarihi a watan Nuwamba.''

A birnin Doha, firaministan Qatar Sheikh Mohammed Bin Abdulrahman al-Thani ya amsa tambayoyi daga manema labarai bayan sanar da yarjejeniyar.

Tambaya ta farko ita ce me yasa sai a yanzu aka cimma yarjejeniyar, kuma shin matsi ne daga shugaban Amurka mai jiran gado ta sa aka cimma yarjejeniyar.

Al Thani ya ce Qatar ta fuskanci wasu abubuwa da suka faru a watannin baya-bayan nan.

''Mun ga matakai da Amurka ke ɗauka a baya-bayan nan da suka taimaka wajen kaiwa ga wannan lokaci,'' in ji shi.

Ya ƙara da cewa abin da suka gani daga Amurka a baya-bayan nan haɗin gwiwa ne da ya zarce na gwamnatocin biyu, wanda ya bayyana a matsayin sadaukarwa domin cimma yarjejeniya.

Ta yaya za a aiwatar da yarjejeniyar?

Firaiministan Qatar, Sheikh Mohammed bin Abdul Rahman Al Thani lokacin da yake jawabi ga manema labarai bayan cimma yarjejeniyar a ranar 15 ga watan Janairun 2025

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Firaiministan Qatar, Sheikh Mohammed bin Abdul Rahman Al Thani lokacin da yake jawabi ga manema labarai bayan cimma yarjejeniyar a ranar 15 ga watan Janairun 2025

Akwai buƙatar majalisar tsaron Isra'ila ta amince da yarjejeniyar ta hanyar kaɗa ƙuri'a, duk da ƙalubalantar matakin da wasu ministoci na ɓangaren gwamnati masu tsattsauran ra'ayi ke yi.

A yayin jawabi ga manema labarai, an tambayi Firministan Qatar din kan irin tabbaci ko yaƙinin da yake da shi cewa yarjejeniyar za ta yi nasara har a wuce mataki na farko.

Ya ce suna da yaƙini kan hakan kuma nasarar ta ta'allaƙa ne kan ɓangarorin biyu.

Da aka tambaye shi kan matakan da aka sanya domin tabbatar da ɓangarorin biyu sun bi sharuɗɗan yarjejeniyar, ya ce ƙasashe uku - Amurka, Masar da Qatar- za su sanya ido kan aiwatar da yarjejeniyar.

''Muna sa ran ɓangarorin biyu za su bi ƙa'idojin yarjejeniyar,'' in ji shi, sai dai ya kuma yi la'akari da cewa irin waɗannan yarjeniyoyin suna da sarƙaƙiya.

Wane ne zai mulki Gaza?

Magoya bayan Isra'ilawan da akai garkuwa da su, ranar 7 ga watan Oktoba 2023 lokacin da Hamas ta kaddammar da hari kan Isra'ila. 'Yan uwan na dauke da ky7andira a lokacin zanga-zangar kiran a kubutar da 'yan uwansu gabannin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas a birnin Tel Aviv, 15 Junairu 2025.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, ..

Ko wane ɓangare ne zai jagoranci Gaza bayan yaƙin?

Wannan tambaya ta kasance ɗaya daga cikin manyan tambayoyin da ba a amsa su ba.

Dole ne hukumomin Falasɗinawa (Palestinian Authority PA) su zama su kaɗai ne gwamnatin da ke da iko a Gaza bayan yaƙin, in ji Firaministan Falasɗinawa, Mohammad Mustafa a ranar Laraba, gabanin sanar da yarjejeniyar tsagaita wutar.

Isra'ila ta ƙi amincewa da barin Hamas ta cigaba da iko da yankin. Ta kuma ƙi amincewa ta bar Gaza ƙarƙashin jagorancin PA, wadda ke jagorantar wani ɓangare na yankunan da Isra'ila ta mamaye a Gaɓar yamma da kogin Jordan.

Kuma Isra'ila na so ta cigaba da yin iko kan tsaron Gaza bayan yaƙin ya kawo ƙarshe.

Sai dai tana aiki tare da Amurka da kuma Haɗaɗɗiyar daular Larabawa domin shirya tsarin samar da gwamnatin riƙon ƙwarya da za ta jagoranci Gaza a yayin da ake sauye-sauye a PA.

Daga nan sai sabuwar gwamnatin ta amshi ragamar mulkin a matsayin gwamnatin dindindin.