Hotunan yadda kungiyar NLC ke gudanar da zanga-zanga a Najeriya

Kungiyar kwadago ta Najeriya ta soma gudanar da zanga-zanga a fadin kasar domin tilasta wa gwamnatin kasar biyan bukatun kungiyar Malaman Jami'o'i ta ASUU.

Hakan na faruwa ne a yayin da aka shiga wata na shida da soma yajin aikin Malaman Jami'o'in sakamakon abin da suka kira kin da Gwamnatin Tarayya ta yi na mutunta yarjejeniyar da suka kulla game da inganta tsarin karatunsu - da suka hada da samar da karin kayan aiki da inganta albashi da alawus-alwasu na Malaman Jami'ar.

Ga wasu hotunan yadda kungiyar ta NLC take gudanar da zanga-zanga:

Wasu 'yan ASUU
Bayanan hoto, A Jihar Kano, tun da sanyin safiya 'yan kungiyar ta NLC suka hallara domin soma zanga-zangar
Kungiyoyi da dama, da ke karkashin NLC, sun amsa kiran shiga zanga-zangar
Bayanan hoto, Kungiyoyi da dama, da ke karkashin NLC, sun amsa kiran shiga zanga-zangar
NLC ta ce abin takaici ne yadda gwamnatin Najeriya take watsi da batun inganta ilimi
Bayanan hoto, NLC ta ce abin takaici ne yadda gwamnatin Najeriya take watsi da batun inganta ilimi
Shugabannin kungiyoyin kwadagon sun sha yin zargin cewa gwamnati ba ta damu da harkar ilimi ba ne saboda 'ya'yan manyan kasar suna karatu a kasashen ketare
Bayanan hoto, Shugabannin kungiyoyin kwadagon sun sha yin zargin cewa gwamnati ba ta damu da harkar ilimi ba ne saboda 'ya'yan manyan kasar suna karatu a kasashen ketare
Gamayyar kungiyoyin farar-hula na cikin wadanda suka bi sahun masu gudanar da tattakin.
Bayanan hoto, Gamayyar kungiyoyin farar-hula na cikin wadanda suka bi sahun masu gudanar da tattakin.