Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Wane yunƙuri ya kamata jagororin PDP su yi don magance matsalolin jam'iyyar?
- Marubuci, Muslim Muhammad Yusuf
- Aiko rahoto daga, Abuja
- Lokacin karatu: Minti 6
Tun bayan wani hukuncin kotu da ya soke babban taron jam'iyar da ya zaɓi Tanimu Turaki a matsayin shugaban PDP a bara, sai jam'iyyar ta sake shiga ruɗani da rashin tabbas.
Hakan na zuwa ne a dai-dai lokacin da babban zaɓen ƙasar na 2027 ke ci gaba da ƙaratowa, sannan kwanaki kaɗan suka rage hukumar zaben kasar INEC ta rufe damar gudanar da zaɓen shugabancin jam'iyyu gabanin bayar da damar fara yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar.
Kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ce dai ta yi watsi da ƙarar da PDPn ta ɗaukaka a ranar 31 ga watan Oktoban 2025, inda alƙalin babbar kotun tarayyar ƙasar James Omtosho ya dakatar da hukumar zaɓe ta ƙasar daga amincewa da duk wani mataki da ya fito daga taron na jam'iyar a Nuwamban 2025.
Kotun ta ce ƙarar da PDP ta ɗaukaka ba ta da wata amfani kuma hukuncin da kotun baya ta yanke yana kan daidai.
Tuni tsagin da ke samun goyon bayan ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike ƙarƙashin shugabancin Abdurrahman Muhammad suka fara yunƙurin shirya wani sabon zaɓen shugabannin jam'iyar.
Sai dai tsagin Tanimu Turakin sun ce za su tunkari kotun kolin kasar, kan hukuncin da kotun ta yanke.
Wannan lamari ya sa dattawan jam'iyar ke ba da shawarar ya kamata kowane ɓangare ya yi la'akari da hanyar da za ta samar da masalaha.
Shawarar da Bukola Saraki ya bayar kan rikicin PDP
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Bukola Saraki, ya bayyana matsayarsa kan rikicin jam'iyyar bayan hukunce-hukuncen kotu da suka shafi jagorancinta.
A wata sanarwar da ya fitar, Saraki ya buƙaci shugabanni da masu ruwa da tsaki na PDP da su rungumi hukuncin kotun ɗaukaka ƙarar, wanda ya soke taronta na Ibadan da kuma jagorancin da aka zaɓa a baya, inda ya buƙaci a bi ƙa'idojin da doka ta gindaya.
Ya jaddada buƙatar yin sulhu tsakanin ɓangarorin don tabbatar da cewa PDP ba ta wargaje ba, musamman yayin da take shirin tunkarar zaɓen 2027.
Saraki ya ba da shawarar a gudanar da sabon babban taro na ƙasa wanda zai bi dukkanin ƙa'idojin da hukumar zaɓe ta INEC ta gindaya.
"A bayyane yake cewa ba mu da lokacin ɓatawa wajen jiran hukuncin kotun ƙoli. Idan ba haka ba, ba za mu iya kammala shirye-shiryen da suka kamata wajen fidda ɗantakara a kan lokaci ba," in ji shi.
Saraki ya jaddada cewa, duk da rikicin da ke cikin jam'iyar, PDP ba za ta mutu ba kuma za ta shiga zaben 2027, amma dole ne a ɗauki mataki kan lokaci.
Saraki ya ce idan har dukkanin ɓangarorin ba su abin da ya dace ba, ko suka nace sai sun tunkari kotun ƙoli, hakan zai haifar musu da tsaiko wajen shirya wa zaɓen 2027, musamman ganin yadda ƴan takara ke ɗari-ɗarin neman wata kujera a jam'iyar saboda abin da ka iya zuwa ya dawo na shari'a.
Me tsagin Wike suka ce?
Ɓangaren da ke samun goyon bayan gwamnonin PDP da wanda ke biyayya ga Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, sun nuna ƙwarin gwiwar cewa hukuncin kotu zai yi musu daɗi.
Sakataren yaɗa labarai na kwamitin riƙon ƙwarya ƙarƙashin Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu, waɗanda Wike ke goyon baya, Muhammad Jungudo Haruna, ya ce lokaci ya yi da kowa zai kai zuciya nesa idan har ana son ci gaban jam'iyar ne.
Ya ce shawarar da jagororin jam'iyar suka bayar ya zo a kan gaɓa kuma sun kira ga ɗaya ɓangaren da su zo a haɗa kai domin ci gaban PDP.
Ya ce: "Mun ɗauki matakai ne wajen gudanar da dukkannin abubuwa da kotu ta ce sai an yi kafin tunkarar zaɓe."
Jangudo ya ce za su ci gaba da shugabancin jam'iyar har zuwa lokacin da matsayin wannan kotun ya sauya.
"Ita INEC tana amfani ne da hukuncin kotu. Hukuncin kotu kuma a rana mai kamar ta yau ta ayyana, ta umurci hukumar zabe da ta yi mu'amala da shugabanci na riƙon ƙarya karkashin Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu," in ji Jungudo.
Tsagin Tanimu Turaki sun dage kan zuwa kotun ƙoli
Sai dai tsagin shugabancin Tanimu Turaki sun nace cewa su ne halastattun shugabanni a jam'iyar ta PDP kuma za su tafi kotun ƙoli domin ta taɓa yanke irin wannan hukunci a baya.
Sanata Umar Tsauri, ɗaya ne daga cikin kwamitin amintattu na jam'iyar da ke goyon bayan Tanimu Turakin, ya ce babu wata alama da ke nuna ba su ke kan daidai ba.
Ya ce salon da tsagin su Wiken suka ɗauka ba zai haifar da ɗa mai ido ga jam'iyar ba, kasancewar sun nuna goyon bayansu ga sake zaɓen shugaban ƙasa Bola Tinubu a 2027 duk da suna jam'iyar adawa.
"Idan ka ce a yi sulhu, to da wa za a yi? Shugabancin da ake so a yi yanzu, ba wanda zai tsaya takara a PDP ko kansila ne," in ji Sanata Tsauri.
"Muna so shugabacin da zai ba PDP gashin kanta, ta tsaida ɗantakara wanda take so a lokacin da take so."
Sanata Tsauri ya ce za su tabbatar da cewa sun dawo jam'iyar kan tsarin da ya dace da ita a matsayin babbar jam'iyar adawa.
Abin da ya kamata PDP ta yi
Masana siyasa na ganin ya zama wajibi PDPn ta yi karatun ta natsu domin daidaita rikicin da ya dabaibaye ta a kan lokaci.
Dr. Ibrahim Baba, mai sharhi kan lamuran siyasa daga jami'ar Usmanu Danfodio, ya ce idan har jagororin jam'iyar na son ci gaba dole su cire son rai kuma su haɗa kansu waje guda.
Ya yi gargaɗin cewa idan ba su yi abin da ya dace ba, akwai yiwuwar jam'iyar za ta watse ba da daɗewa ba.
Dr. Baba ya ce: "Babban makami wanda ya rage a hannun waɗannan masu ruwa da tsaki na jam'iyar shi ne su kauda ra'ayoyin kawunansu."
"Su haɗa ƙai domin ganin sun samu sulhu domin samar da shugabanci karɓaɓɓe ga mambobinta."
Masanin ya ƙara da cewa jam'iyar adawar na fuskantar babban ƙalubale gabanin zaɓen 2027 da ke tafe, saboda ba su da isasshen lokaci a yanzu.
"Dole ne su yi shiri tun da wuri," in ji shi.
"Idan aka ci gaba a haka, za su samu kansu a yanayin da jam'iyar za ta ruguje. Idan ma ba ta ruguje ba, wasu mambobinta za su riƙa ƙokarin haifar mata da matsala don ganin ba ta yi nasara ba." in ji Dr. Baba
Ko a jikinmu - Makinde
Gwamnan jihar Oyo Seyi Makinde ya ce ko kaɗan ba su damu ba, duk da su biyu kawai suka rage a matsayin gwamnonin PDP.
A yayin da yake jawabi ga kwamitin amintattu na jam'iyar a Abuja, Makinde ya ce abin da yake faruwa a PDP babban ƙalubale ne ga jagororinta da kuma dimokraɗiyyar Najeriya.
Makinde ya ce mutane da dama na mamakin salon siyasar Najeriya, da yadda lamura ke tafiya.
"Mu biyu kaɗai muka rage. Ba mu damu ba," in ji shi.
"Duk abin da za mu yi a matsayin jam'iya, ya zama wajibi mu kula saboda tarihi ba zai mance da abin da muka yi ba."
A yanzu dai gwamnoni biyu suka rage a PDP bayan gwamnan Zamfara Dauda Lawal ya ayyana ficewa zuwa APC.
A halin yanzu jam'iyyar APC mai mulki na da gwamnoni 31 cikin jihohin ƙasar 36.
Sauran gwamnonin hamayyar biyar da suka rage wa jam'iyyun hamayya biyu na PDP ne yayin da AP da APGA da LP kowacce na da ɗaya.
Tushen rikicin shugabancin jam'iyyar PDP
Rikicin jam'iyar PDP ya samo asali ne tun a ranar 15 ga watan Nuwamban 2025, inda gwamnonin jam'iyar suka amince da babban taron da suka yi a Ibadan wanda ya samar da Turaki a matsayin shugaban jam'iyar na tsawon shekaru huɗu.
Gwamnonin sun kuma jagoranci miƙa mulki daga tsohon shugaban riƙon ƙarya, Umar Damagum, zuwa ga Turaki kafin wa'adin Damagum ya ƙare ranar 9 ga Disamban 2025.
A ɗaya ɓangaren kuma, da ke biyayya ga Ministan Abuja sun kafa kwamitin riƙon ƙarya na mutane 13 ranar 8 ga Disamban 2025, inda suka naɗa Abdulrahman a matsayin shugaban riƙon ƙarya na tsawon kwanaki 60.