Ƴan wasan da suka fi zura ƙwallo a Gasar Kofin Afirka ta 2025

xxx

Asalin hoton, Getty Images

Lokacin karatu: Minti 2

An kammala Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa ta nahiyar Afirka ta 2025 wadda ta gudana a ƙasar Moroko.

An buga wasan ƙarshe mai zafi tsakanin Senegal da mai masaukin baƙi Moroco a ranar Lahadi 18 ga watan Janairun 2026.

Ƙwallon da Pape Gueye ya ci a cikin ƙarin lokaci ita ce ta raba gardama, inda aka tashi: Senegal 1-0 Moroko

Ga jerin ƴan wasan da suka fi zura ƙwallo daga farkon gasar zuwa ƙarshe:

  • Brahim Díaz (Moroko): Ƙwallo - 5
  • Victor Osimhen (Najeriya): Ƙwallo - 4
  • Mohamed Salah (Masar): Ƙwallo - 4
  • Ademola Lookman (Najeriya): Ƙwallo - 3
  • Ayoub El Kaabi (Moroko): Ƙwallo - 3
  • Amad Diallo (Ivory Coast) - Ƙwallo - 3
  • Riyad Mahrez (Aljeriya): Ƙwallo - 3
  • Lassine Sinayoko (Mali): Ƙwallo - 3
  • Pape Gueye (Senegal): Ƙwallo - 3

Bayan nan akwai ƴan wasa 14 waɗanda suka zura ƙwallo bibbiyu daga farkon gasar, kamar irin su R. Onyedika da Addams A na Najeriya da C. Ndiaye na Senegal, da G. Kakuta na DR Congo da dai sauran su.

Sai kuma ƴan wasa 57 waɗanda suka zura ƙwallo ɗaɗɗaya, kamar Pierre-Emerick Aubameyang na Gabon, da Wilfred Ndidi na Najeriya da sauran su.

Taimakawa a zura ƙwallo

Ɗan wasan Najeriya Ademola Lookman ne ya fi yawan taimakawa a zura ƙwallo, inda ya taimaka sau huɗu.

Daga nan sai ɗan wasan Senegal, Sadio Mane, wanda ya taimaka aka zura ƙwallo uku.

Akwai kuma wasu ƴan wasa 12 da suka taimaka sau bibbiyu wajen zura ƙwallo, kamar Victor Osimhen da Adams Akor na Najeriya.