Majalisar Tarayyar Turai ta amince da wani kuduri da ke kira ga Hukumar Tarayyar Turai da ta dakatar da tallafin kuɗi kai tsaye ga gwamnatin Tanzania, inda ta yi nuni da kisan gillar da aka yi bayan zaɓe da kuma take haƙƙin ɗan adam.
A wani kuduri daban da ba lallai ne ya yi wani tasiri ba, Ƴan Majalisar sun bukaci Hukumar da ta janye daftarin shawarar da ta yanke don ba da kuɗi ga wani shirin samar da ci gaban kasa na shekara-shekara na EU na 2025 ga Tanzania.
Ƴan Majalisar sun yi Allah wadai da abin da suka bayyana a matsayin amfani da ƙarfi kan masu zanga-zanga bayan zaɓen shugaban kasar na watan Oktoban da ya gabata, tashin hankalin da aka ruwaito ya yi sanadiyyar mutuwar ɗaruruwa da kuma jikkatar wasu da dama.
An ayyana Shugaba Suluhu a matsayin wadda ta lashe zaɓen da kashi 98% na ƙuri'un da aka kaɗa, wanda hakan ya sa 'yan adawa suka ƙi amincewa da shi, tare da bayyana shi a a matsayinwani "izgili ga dimokuraɗiyya."
Yanzu dai, Majalisar Tarayyar Turai ta yi kira ga hukumomin Tanzania da fara gudanar da tattaunawar siyasa da 'yan adawa, da ƙungiyoyin fararen hula da wakilan waɗanda abin ya shafa don ƙoƙarin warware rikicin da kuma shirya wani zaben da za a yi adalci.
Ƴan Majalisar sun ƙara yin Allah wadai da "tsare shugaban 'yan adawa Tundu Lissu da aka yi bisa dalilai na siyasa" inda ake tuhumarsa da laifin cin amanar ƙasa, laifin da idan aka same shi da shi, zai iya fuskantar hukuncin kisa.
Ƴan majalisar sun kuma matsa lamba kan a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma ba tare da nuna son kai ba kan zargin kashe-kashen da ake yi, bacewar da aka tilasta wa mutane, azabtarwa da sauran cin zarafi.
Jam'iyyun adawa da Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan adam sun yi zargin cewa jami'an tsaro sun kashe ɗaruruwan masu zanga-zanga kuma sun kwashe gawawwakin mutane zuwa wurare da ba a bayyana ba.