Kotu ta ba da belin Malami

Asalin hoton, Abubakar Malami
Babbar kotun tarayya da ke Abuja ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Joyce Abdulmalik, ta amince da belin tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami tare da ɗansa Abdulaziz Malami, kan kuɗin naira miliyan 200,
Sai dai kotun ta umarce su da a tsare su a gidan yarin Kuje har sai sun cika sharuddan belin da aka gindaya musu.
Mai shari’ar ta bayar da belin ne bayan ta saurari hujjojin neman beli da lauyansu, Joseph Daudu ya gabatar.
Kotun ta ce dole ne kowannensu ya gabatar da mutane biyu a matsayin masu tsaya musu, inda ɗaya daga cikinsu dole ne yana da fili a unguwar Maitama ko Asokoro.
Haka kuma sai an ajiye takardun mallakar filin tare da fasfo din masuntsaya musu a wurin Mataimakin Magatakardan kotu.
Kotun ta kuma umarci Malami da ɗansa su miƙa fasfonsu da hotunansu ga kotu.
An sanya ranar 4 ga Maris domin fara shari’ar.
Hukumar tsaro ta farin kaya,DSS ce ta gurfanar da su kan tuhume-tuhume guda biyar da suka shafi zargin tallafawa ta’addanci da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.














