KAI TSAYE, Labaran wasannin BBC Hausa kai-tsaye 4-10 Janairu, 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa kai-tsaye daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Janairu, 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammed Abdu, Haruna Kakangi

  1. Neymar

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan Brazil, Neymar, ya tsawaita kwantiraginsa da Santos har zuwa ƙarshen kakar 2026, yayin da yake ƙoƙarin ganin an gayyace shi gasar cin kofin duniya.

    Ɗan wasan mai shekaru 33, wanda ya koma ƙungiyar da ya fara yiwa tamaula tun yana matashi, bai buga wa Brazil wasanni ba, saboda fama da jinya.

    Tsohon ɗan wasan Barcelona da Paris St-Germain ya na buga wasanni duk da raunin da yake ɗauke da shi domin taimaka wa Santos wadda ba ta faɗi ba daga babbar gasar Brazil a kakar da ta wuce, inda ya zura ƙwallaye biyar a wasa biyar na ƙarshe.

    Daga bisani an yi masa tiyata a gwiwar ƙafarsa ta hagu, don ya samu shiga cikin tsare-tsaren kocin Brazil, Carlo Ancelotti, a wannan bazarar.

    Ancelotti ya sanar a watan Oktoba cewa dole ne Neymar — wanda shi ne dan wasan da ya fi kowa zura kwallaye a tarihin Brazil da guda 79 a raga — ya kasance cikin koshin lafiya kuma kan ganiya kafin a sake kiransa.

    Neymar ya shafe wata 12 ba tare da buga wasa ba bayan jijiyar gwiwa a watan Oktoban 2023.

    An shirya zai koma cikin tawagar kasa a bara bayan wata 17 na rashin buga wasa, amma an tilasta masa janyewa daga tawagar sakamakon raunin da ya ji.

    Brazil za ta kara da Scotland da Morocco da Haiti a rukuni na uku a gasar cin kofin duniya, wadda za ta fara wasa a ranar 11 ga watan Yuni a wasanin da za a yi haɗaka a Amurka da Canada da kuma Mexico.

  2. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Newcastle United za ta yi gogayya da Tottenham idan ta koma wurin kungiyar Wolves a kokarin da take yi domin siyan dan wasan NorwayJorgen Strand Larsen mai shekara 25. (ChronicleLive)

    Tottenham za ta sayi wani sabon dan wasan gaba a watan nan na Janairu saboda raunin da dan wasan Ghana Mohammed Kudus, mai shekara 25 ya ji , ya yi muni fiye da yadda suka yi tunani tun farko. (Telegraph)

    Darektan kungiyar Roma, Ricky Massara ya ce halin da ake ciki game da duk wani yunkuri na siyan dan wasan gaban Manchester United Joshua Zirkzee, mai shekara 24, ya sauya saboda korar da aka yi wa kocin kungiyar ta Old Trafford, Ruben Amorim (Sky Sports)

    Fatan da Juventus take da shi na siyan dan wasan Italiya Federico Chiesa, mai shekara 28, daga Liverpool ya dogara ne kan ko dan wasan Masar Mohamed Salah, mai shekara 33, zai ci gaba da taka leda a Anfield. (La Gazzetta dello Sport)

    Ita ma Napoli na son Chiesa sai dai Liverpool ba ta sami wani tayi a hukumance ba daga wata kungiya ba kuma abu ne mai wuya ta sayar da shi a watan Janairu. (Sky Sports News)

  3. Za a bayar da ladan Dalar Amurka miliyan 75 a Australia Open, Australian Open

    US Open

    Asalin hoton, Getty Images

    An ƙara kuɗin kyautar lashe gasar Australian Open ta bana da kashi 16 cikin 100 zuwa dalar Amurka miliyan 111.5, wanda ya sa ya zama mafi girman kuɗin lada a tarihin gasar, kamar yadda masu shirya gasar suka sanar a ranar Talata.

    Duk namji da macen da za ta lashe kofin bana za su karɓi kowannensu dalar Amurka miliyan 4.15, wanda ya haura dala miliyan 3.5 miliyan da Jannik Sinner da Madison Keys suka samu a bara.

  4. Yadda aka samu takwas da za su kara a ƴan takwas a Afcon, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    An kammala wasannin zagayen ƴan 16 a gasar cin kofin Afirka da ake yi a Moroko.

    Tawagogin ƙasashe sun yi fafatawa mai zafi, an nuna bajinta da kuma ƙwarewa.

    Yanzu dai daga cikin ƴan 16, ƙasashe takwas sun fice daga gasar yayin da takwas suka tsallaka zuwa zagayen kwata-fainal.

    Za a fara gwabzawa a zagayen na kwata-fainal ne ranar Juma'a, 9 ga watan Janairun 2026.

    Mun yi duba kan ƙasashe da za su fafata da kuma abin da ake sa ran gani.

  5. Ten Hag zai koma aiki a tsohuwar ƙungiyarsa, FC Twente, FC Twente

    Ten Hag

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon kociyan Manchester United, Erik ten Hag zai sake komawa tsohuwar kungiyarsa FC Twentae a matakin daraktan tsare tsare daga farkon kakar badi - kamar yadda yadda aka sanar ranar Laraba.

    Ya kuma sa hannun kan yarjejeniyar zuwa karshen kakar 2028 a kungiyar da ya fara taka leda daga 1989 zuwa 2002.

    Kenan mai shekara 55 zai fara aiki daga 1 ga watan Fabrairu, zai maye gurbin Jan Steuer, wanda ya ajiye aikin.

  6. Jones ta kai kwata fainal a ATP a Aucland, Ƙwalon tennis

    Ƴar Burtaniya, Francesca Jones ta kai zagayen kwata fainals bayan doke Sinja Kraus a ATP a Aucland.

    Tana buga wasannin ne domin shirin buga gasar Australian Open da za a fara 18 ga watan nan na Janairu.

  7. An samu tawaga takwas da za ta buga kwata fainals a Afcon, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Ranar Talata aka kammala wasannin zagaye na biyu a babbar gasar tamaula ta Afirka da ake yi a Morocco.

    Tawagar da ta kai zagaye na uku a babbar gasar tamaula ta Afirka ta hada da mai masaukin baki Morocco da Kamaru da Mali da Senegal da Masar da Aljeriya da Najeriya da kuma mai rike da kofin Ivory Coast.

    Kuma daga cikinsu Mali ce ba ta taba lashe Afcon ba, amma a tsakaninsu suna da kofi 22.

    Cikin takwas da za su buga kwata fainal biyar daga ciki za su wakilci Afirka a gasar kofin duniya a bana da ya hada da Morocco da Senegal da Masar da Aljeriya da kuma Ivory Coast.

    Zuwa wannan matakin an buga wasa 44 da cin kwallo 109, Brahim Diaz na Morocco ne kan gaba mai hudu a raga.

    Sai a ranar Juma'a zuwa Asabar za a buga wasannin kwata fainals.

    Za a kara tsakanin Mali da Senegal da na Kamaru da Morocco.

    Sannan Najeriya da Aljeriya da na Masar da Ivory Coast.

  8. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Dan wasa mai kai hari na Poland Robert Lewandowski ba ya son ya bar Barcelona a watan Janairu duk da cewa akwai kungiyoyi da dama da ke zawarcin dan wasan mai shekara 37. (Sky Sports)

    Bayern Munich ta tsawaita kwantaragin dan wasan bayan Faransa Dayot Upamecano, mai shekara 27 wanda wa'adinsa a kungiyar zai kare a bazara. (Sky Sports)

    AC Milan na zawarcin dan wasan Bayern Munich Kim Min-jae, mai shekara 29, sai dai za ta nemi taimakon kungiyar ta Jamus ta bada gudummawa kan albashin dan wasan kasar Koriya ta Kudu domin su iya kulla yarjejeniya. (La Gazzetta dello Sport)

    Dan wasa mai kai hari na Real Madrid, Endrick mai shekara 19 wanda ya je Lyon a matsayin aro ya ce kocin Brazil Carlo Ancelotti ne ya ba shi shawarar barin kungiyar ta Sifaniya domin ya kara samun kwarewa wajen buga tamaula . (Goal)

    Yarjejeniyar da Leicester City ta gabatar wa dan wasa mai kai hari Michail Antonio, kuma tsohon dan wasan West Ham, ta wargaje sakamakon raunin da ya ji. Dan wasan Jamaica mai shekara 35 bai buga wasa ba tun bayan hadarin motar da ya yi a watan Disambar 2024, amma yana tattaunawa kan kwantaragin gajeren zango (Talksport)

    Dan wasan Koriya ta Kudu Yang Min-hyeok, mai shekara 19, na gab da komawa South Coventry City a matsayin aro daga Tottenham. (Fabrizio Romano)

  9. Wasannin Premier League mako na 21 da za a buga, Premier League

    Premier League

    Asalin hoton, Getty Images

    Ranar Laraba, 07 ga watan Janairu

    • Bournemouth da Tottenham
    • Brentford da Sunderland
    • Crystal Palace da Aston Villa
    • Everton da Wolves
    • Fulham da Chelsea
    • Manchester City da Brighton
    • Burnley da Manchester United (20:15)
    • Newcastle United da Leeds United (20:15)

    Ranar Alhamis, 08 ga watan Janairu

    • Arsenal da Liverpool (20:00)
  10. Watakila a bai wa Carrick da Solskjaer aikin riƙon ƙwarya a United, Manchester United

    Man United

    Asalin hoton, Getty Images

    Michael Carrick da Ole Gunnar Solskjaer suna gaba-gaba a matsayin ƴan takarar neman kocin riƙon ƙwarya a Manchester United har zuwa ƙarshen kakar bana.

    Tsoffin ƴan wasan United biyu, waɗanda sun taɓa horar da ƙungiyar a baya, ana sa ran za su tattaunawar kai tsaye da shugabancin ƙungiyar Old Trafford.

    Watakila su yi aikin tare, domin Carrick ya taka muhimmiyar rawa a cikin masu horarwa a lokacin da Solskjaer ya maye gurbin Jose Mourinho a Old Trafford a 2018.

    Darren Fletcher, kocin matasan United ƴan kasa da shekara 18, shi ne aikin riƙon ƙwarya, kuma shi ne zai ja ragamar ƙungiyar a wasan Premier League da Burnley ranar Laraba.

    Ana kuma cewa Ruud van Nistelrooy, tsohon ɗan wasan gaba na United, zai kasance shima a cikin ƴan takara.

    An koro Amorim a ranar Litinin bayan watanni 14 yana horar da United cikin ɗan karen kalubale.

    United na shirin naɗa sabon koci na dindindin da zai maye gurbin Amorim da zarar an kammala kakar bana.

    Solskjaer ya fara jagorantar ƙungiyar a irin wannan yanayi ne lokacin da United ta sallami Mourinho a 2018, daga bisani kuma aka ba shi cikakken aikin horarwa na tsawon shekaru uku kafin a sallame shi a watan Nuwamba 2021.

    Carrick daga baya ya jagoranci ƙungiyar wasa uku a matsayin kocin wucin gadi bayan sallamar Solskjaer, kafin ya bar United a watan Disamba 2021.

    Tsohon ɗan wasan tsakiyar Ingila ba shi da wata ƙungiyar da yake horarwa tun bayan da aka sallame shi daga ƙungiyar Championship, Middlesbrough, a watan Yuni da ya gabata bayan shekaru biyu da rabi yana jagoranci.

    An sallami Solskjaer daga ƙungiyarsa a Turkiyya, Besiktas, a watan Agusta.

    Kocin Crystal Palace, Oliver Glasner, da tsohon kocin Brighton, Roberto de Zerbi — wanda yanzu yake horar da Marseille — an fahimci suna cikin ƴan takara.

  11. Kokarin da Burkina Faso ke yi a Afcon a tarihi, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    • Ta kawo wannan gurbin ne, bayan nasara a kan Equatorial Guinea da Sudan, sannan Algeria ta doke ta.
    • Ta haura matakin zagaye na biyu a 2021, amma aka yi waje da ita a irin wannan matakin a 2013.
    • A wasan farko a zagayen ƴan 16 a 2021 ta fara yin 1-1 da Gabon har da karin lokaci daga baya ta yi nasara 7-6 a bugun fenariti.
    • Sai ta yi rashin nasara 2-1 a hannun Mali a zagayen ƴan 16 a 2023.
    • Idan ta yi nasara za ta kara a karo na biyar a kwata fainal (1998, 2013, 2017 da kuma 2021).
    • Dukkan wasan da ta buga zagayen ziri ɗaya kwale ba ta tashi 0-0
    • Issoufou Dayo da Hervé Koffi da Arsène Kouassi da kuma Edmond Tapsoba sun buga wa Burkina Faso dukkan karawa uku ta cikin rukuni a Afcon a Morocco.
  12. Bajintar da Ivory Coast ke yi a gasar kofin Afirka, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    • Ta kawo wannan matakin bayan nasara a kan Mozambique da Gabon da yin canjaras da Kamaru.
    • Karo na huɗu kenan a baya-bayan nan da za ta fafata a zagaye na biyu - a baya ta kai wannan gurbin a 2019 da 2023 daga baya aka yi waje da ita a 2021.
    • Wadda take rike da kofin ba ta yin nasara a zagayen ƴan 16 a Afcon tun bayan Masar da ta yi wannan bajintar a 2010.
    • Tun daga 2010, duk wadda take rike da Afcon ba ta iya zuwa matakin kwata fainal tun daga Zambia (2013) da Ivory Coast (2017) da Kamaru (2019) da Algeria (2021) da kuma Senegal (2023).
    • A matakin mai rike da Afcon, karo na biyu kenan da Ivory Coast ke haura matakin karawar cikin rukuni, bayan 2017 da take da Afcon.
    • Idan har ta yi nasara za ta kai kwata fainal a Afcon karo na 12 jimilla (1992, 1994, 1998, 2006, 2008, 2010, 2012, 2013, 2015, 2019 da kuma 2023).
    • Amad Diallo ya ci ƙwallo biyu a Morocco, watakila ya zama ɗan kasar na farko da zai zura uku ko fiye da haka a gasa, bayan kwazon Didier Drogba a 2012.
    • Ba a doke koci, Emerse Faé ba a wasannin Afcon, tun bayan da aka bashi aikin, ya ja ragamar wasa bakawi da cin biyar da canjaras biyu.
  13. Super Eagles za ta kara tsakanin Aljeriya ko Dr Congo, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Tawagar Najeriya ta kai kwata fainal a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Morocco ranar Litinin.

    Ta kuma kai zagayen gaba, sakamakon doke Mozambique 4-0, ita ce ta farko da ta ci ƙwallo huɗu a wasannin bana, kuma tana da 12 yayin da huɗu suka shiga ragarta.

    Za ta kara a zagayen ƴan takwas da duk wadda ta yi nasara tsakanin Aljeriya ko kuma Jamhuriyar Congo.

  14. Evans zai koma United domin ya taimakawa Fletcher, Manchester United

    Evans

    Asalin hoton, Getty Images

    Jonny Evans zai sake komawa Manchester United domin ya taimakawa kociyan rikon kwarya, Darren Fletcher gudanar da aiki.

    Ita kuwa West Bromwich Albion na neman sabon kociya, bayan da ta kori Ryan Mason.

  15. West Ham za ta soke kwantiragin da ta rage tsakaninta da Wilson, West Ham United

    Callum Wilson

    Asalin hoton, gett

    West Ham na dab da cimma yarjejeniya da ɗan Callum Wilson domin kawo ƙarshen kwantiraginsa da ta rage a tsakaninsu.

    Wilson ya koma West Ham, bayan da ƙwantiraginsa ya kare a Newcastle United a karshen kakar da ta wuce, wanda ya ci ƙwallo huɗu a wasa 18 a West Ham.

    Za a kai ga wannan matsaya, saboda ba zai ke samun buga wasanni da yawa ba, sakamakon sayen ƴan wasa, Pablo Felipe da Taty Castellanos da ta yi a wannan watan.

    Wilson mai shekaru 33 yana son ci gaba da buga tamaula akai-akai.

    Saboda haka, ana sa ran Wilson zai bar Hammers, inda majiyoyi suka tabbatar da cewa tattaunawa kan an kusan kammala kawo karshen yarjejeniyar da ta rage masa a ƙungiyar.

  16. , Daga Jaridu

    Rashford

    Asalin hoton, Getty Images

    Korar da aka yi wa kocin Manchester United, Ruben Amorim za ta iya ba dan wasan Ingila Marcus Rashford, mai shekara 28, wanda ke zaman aro a Barcelona, hanyar komawa Old Trafford.(Mirror)

    Watakila Oliver Glasner na cikin wadanda Man U ke so su maye gurbin Amorim da ta kora.

    Shugabanin United na kaunar Glasner, dan kasar Australia mai shekara 51,wanda kwantaraginsa da Crystal Palace zai kare a bazara (Telegraph)

    Ita ma Fulham na jiran Manchester United ta tuntube ta kan kocinta, Marco Silva, dan kasar Portugugal. (Sun)

    Dan wasan tsakiya na Ingila Kobbie Mainoo, mai shekara 20 da dan wasan Netherlands Joshua Zirkzee, mai shekara 24, da kuma dan wasan tsakiya na Uruguay Manuel Ugarte, mai shekara 24, duk sun nuna alamun barin Manchester United a watan Janairu idan Amorim ya zauna. (Mail)

    Juventus ta fara tattaunawa da Liverpool kan batun bada aron Federico Chiesa, inda dan wasan na Italiya mai shekara 28 ya nuna alamun yana son ya koma kungiyar ta Seria A inda ya shafe kaka biyu tsakanin 2022-2024. (La Gazzetta dello Sport)

    Bournemouth ta shirya biyan Yuro miliyan 40 don siyan dan wasan Stuttgart da Jamus Jamie Leweling a matsayin wanda zai maye gurbin dan wasan Ghana Antoine Semenyo mai shekaru 25, wanda ke dab da komawa Manchester City, amma kungiyar ta Bundesliga ta yi watsi da tayin na Cherries.(Sky Sports )

  17. Ruben Dias zai yi jinyar mako shida a Man City, Manchester City

    Ruben Dias

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan Manchester City, Ruben Dias zai yi jinyar mako shida, kamar yadda koci Pep Guardiola ya sanar.

    An sauya shi sakamakon raunin da ya ji a wasan Premier League da suka tashi 1-1 da Chelsea a ranar Lahadi.

    Ranar Litinin aka sanar da Josko Gvardiol, zai yi dogon jinya bayan da ya karya ƙafa, haka kuma John Stone har yanzu bai murmure ba.

    Rayan Aït-Nouri yana buga gasar kofin nahiyar Afirka, yayin da Nathan Aké bai koma kan ganiya ba..

    Wannan halin da ake ciki watakila Manchester City za ta nemi ɗan baya a wannan wata, kuma an ruwaito cewa Marc Guéhi na Crystal Palace yana cikin jerin ƴan wasan da take son saya.

    Ana kuma ganin cewa City na dab da kammala yarjejeniya da ɗan wasan Bournemouth, Antoine Semenyo, domin ya koma Etihad da taka leda.

    John Stones dai ya shafe wata guda yana jinya.

  18. Maresca ya yi ban kwana da magoya bayan Chelsea cikin ban tausayi, Chelsea

    Maresca

    Asalin hoton, Getty Images

    Enzo Maresca ya yi ban kwana da magoya bayan Chelsea cikin ban tausayi a ranar Talata, inda ya ce ya cimma duk abin da zai iya a cikin wata 18 da ya yi yana jagorantar ƙungiyar, bayan da aka kore shi ranar 1 ga watan Janairu.

    Kocin ɗan Italiya shi ne na baya-bayan nan da ya shiga cikin jerin sauye-sauyen masu horaswa a Chelsea ƙarƙashin mallakar BlueCo, bayan wasa ɗaya kacal da ya ci a cikin bakwai a Premier League da ta kai mahukuntan suka ɗauki matakin rabuwa da shi.

    A ƙarƙashin jagorancinsa, Chelsea ta lashe gasar Conference League da Fifa Club World Cup, sannan ta samu tikitin shiga gasar Champions League a kakar bara — karo na farko cikin shekaru biyu — amma kocin ɗan Italiya bai samu cikakken goyon bayan mahukuntan ba.

    Bayan tafiyarsa a makon da ya gabata, an naɗa kocin ƴan ƙasa da shekara 21 na Chelsea, Calum McFarlane, a matsayin rikon kwarya, daga baya aka tabbatar da Liam Rosenior a ranar Talata a matsayin sabon babban kocin Chelsea.

  19. , Daga jaridu

    West Ham

    Asalin hoton, Getty Images

    Dole Chelsea ta dauki mataki cikin gaggawa idan tana son ta sayi dan wasan Rennes Jeremy Jacquet, mai shekara 20, saboda Liverpool da Arsenal da Real Madrid da kuma Manchester United duk suna sha'awar dan wasan na Faransa (Teamtalk)

    Barcelona na son Al-Hilal ta bada aron dan wasan Portugal Joao Cancelo, mai shekara 31, yayin da Inter Milan ke zawarcinsa. (La Gazzetta dello Sport)

    Crystal Palace na shirin fafatawa da West Ham don siyan dan wasan Norway Jorgen Strand Larsen, mai shekara 25, daga Wolves. (Mail)

    Tottenham ta tattauna da Santos kan kulla yarjejeniyar siyan dan wasan Brazil , Souza, mai shekara 19, wanda ke daukar hankalin Newcastle. (Teamtalk)

    Dan wasan Ingila Callum Wilson, mai shekara 33, na tattaunawa da West Ham domin kawo karshen kwantiraginsa bayan ya shafe wata biyar a kungiyar (Athletic)

    Tsohon kocin Wolves Gary O'Neil ya tattauna da Strasbourg kan zama sabon kocinta inda, kocin na kungiyar Faransa na yanzu Liam Rosenior ke cikin wadanda za su iya maye gurbin Enzo Maresca a Chelsea. (Athletic)

    Dan wasan gaban Crystal Palace Romain Esse mai shekaru 20 a duniya ya shirya tsaf domin shafe sauran kakar wasan a matsayin aro a Coventry City.(Sky Sports)

  20. Me Rosenior zai fara fuskanta a Chelsea, Chelsea

    Afcon

    Asalin hoton, BBC Sport

    Da yake Chelsea za ta buga wasan Premier League a gidan Fulham ranar Laraba da daddare, Liam Rosenior ba zai fara aiki a hukumance ba sai karawar FA Cup da Charlton a ƙarshen mako, wato ranar Lahadi, abubuwa na iya sauyawa kafin wasansa na farko a gasar Premier League.

    Musamman ganin cewa maki uku ne ya raba ƙungiya takwas daga Chelsea har zuwa Everton da ke matsayi na 12.

    Amma yanzu, Chelsea tana matsayi na biyar bayan da ta samu maki ɗaya a wasan da ta tashi canjaras da Manchester City, a karkashin jagorancin kocin riƙon ƙwarya, Calum McFarlane.

    Da yake Liverpool da ke matsayi na huɗu za ta je gidan wadda take jan ragamar teburin, Arsenal ranar Alhamis, watakila Rosenior ya kalli wasan da Chelsea za ta je Fulham a Premier League ranar Alhamis.

    Sai dai ana sa ran zai ja ragamar wasa da Chalton a FA Cup zagaye na uku da Premier League da Arsenal da kuma Brentford.