Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 26 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Tinubu ya tsawaita hana fitar da ƙwallon kaɗanya zuwa ƙasashen waje

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tsawaita hana fitar da ɗanyen ƙwallayen kaɗanya zuwa ƙasashen waje da tsawon shekara ɗaya, daga 26 ga Fabrairu 2026 zuwa 25 ga Fabrairu 2027.

    Mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce matakin na nuna ƙudirin gwamnati wajen bunƙasa masana’antu da ƙara darajar kayayyakin cikin gida, da kuma cimma manufofin shirin sabunta fata.

    Sanarwar ta ce manufar tsawaita haramcin ita ce ƙarfafa sarrafa ƙwallon kaɗanya a cikin ƙasa da inganta rayuwar al’ummomin da ke noma ta.

    Domin tabbatar da aiwatar da shirin yadda ya kamata, shugaban ƙasar ya ba da umarni ga ma’aikatu da hukumomi su haɗa kai wajen samar da tsari na ƙasa da zai daidaita manufofin masana’antu da kasuwanci da zuba jari a dukkan sassan harkar kaɗanya.

    Gwamnatin tarayya ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da ke tallafa wa masana’antu na cikin gid tare da samar da ayyukan yi da ƙarfafa matsayin Najeriya a kasuwar kayayyakin noma ta duniya.

  2. An kama ko tsare ’yan jarida 44 a Habasha a shekarar 2025 - Rahoto

    Wani sabon rahoto da ƙungiyar tallafa wa kafafen yaɗa labarai ta Duniya IMS ta fitar ya nuna cewa aƙalla ’yan jarida 44 ne aka sace ko aka tsare a Habasha a shekarar 2025.

    Rahoton ya bayyana cewa an samu ƙaruwar kai wa ƴan jarida hare-hare, da kamun ba gaira ba dalili, da kuma barazanar kuɗi ga ’yan jarida da gidajen watsa labarai.

    Binciken ya nuna cewa matsin lamba kan kafafen yaɗa labarai ya ci gaba kamar yadda aka gani a 2024, lokacin da aka daure ’yan jarida 43.

    Kungiyar ta bayyana shekarar 2025 a matsayin lokaci mai matuƙar damuwa ga ’yan jaridar ƙasar, sakamakon yawaitar tsare-tsare da sace-sace da muzgunawa da suke fuskanta.

    Rahoton ya kuma bayyana irin haɗurran da sassa daban-daban na kafafen watsa labarai ke fuskanta yayin da suke aiki a yanayi mai ƙara zama haɗari, wanda matsalolin siyasa da dokoki da tsaro, da tattalin arziki ke haddasawa.

  3. Gwamnatin Jigawa za ta karɓi Walida daga hannun DSS

    A yau ne ake sa ran gwamnatin jihar Jigawa za ta karɓi Walida Abdulhadi ƴar asalin jihar, wadda ake zargin wani jami'in DSS ya sace ta tare da sauya mata addini daga hannun hukumar DSS.

    Wannan na zuwa ne bayan cimma matsaya a tattaunawar ƙarshe da aka gudanar cikin dare tsakanin hukumomin da abin ya shafa.

    Sakataren yaɗa labaran gwamnatin jihar, Hamisu Muhammad Gumel, ya shaida wa BBC cewa DSS ta amince da miƙa yarinyar a daren Laraba ga gwamnatin jihar dalilin da ya saka Walida ta saka kwana a hannun DSS har zuwa lokacin da gwamnan jihar zai karɓe ta a hukumance.

    A cewarsa, “an amince cewa gwamnatin Jigawa za ta karɓe ta a yau Alhamis."

    Ya ce "mataki na farko bayan karɓar Walida shi ne kai ta asibiti domin a duba lafiyarta, sannan daga baya a tsara yadda za a haɗa ta da iyayenta tare da ɗaukar sauran matakan kulawa da suka dace."

    Lamarin Walida ya jawo hankalin jama’a a faɗin ƙasar, inda ƙungiyoyin farar hula ke ta kira da a yi mata adalci.

    Tun da farko an zargi wani jami’in DSS da sace ta daga Jigawa tare da tilasta mata aure har ta haihu da kuma sauya mata addini.

    A watan da ya gabata ne wata kotu ta bayar da umarnin a sake ta a haɗa ta da iyayenta, umarni da ake ganin matakin yau na karɓarta zai tabbatar da aiwatar da shi.

  4. An zargi Amurka da hana gwamnatin Venezuela biyan kuɗin kare Maduro a kotu

    Lauyan hamɓararran shugaban Venezuela, Nicolas Maduro, ya zargi mahukuntan Amurka da toshe duk wata hanya da gwamnatin Venezuela zata biya kuɗaɗen shari'a ga wanda ya ke karewa.

    Ana dai tsare da Maduro da mai ɗakinsa ne a wani gidan yari da ke New York bisa laifin safarar miyagun ƙwayoyi.

    Cikin wata wasiƙa da ya rubutawa kotu, lauyan Barry Pollack, ya ce tun da farko baitul malin ƙasar ta amince da biyan kuɗaɗen amma daga bisani sai ta janye ba tare da wani bayani ba.

    Ya ce rashin bayar da dama a biya kudaden ya sabawa dokokin shari'a. Mr Maduro da mai dakinsa sun musanta tuhume tuhumen da ake musu.

  5. Tinubu ya buƙaci majalisa ta gyara ƙundin mulki domin kafa ‘yansandan jihohi

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci shugabannin Majalisar Dattawa su fara nazarin yiwuwar gyaran ƙundin tsarin mulki domin samar da dokar da za ta ba da damar kafa ‘yansandan jihohi, a wani yunkuri na magance matsalolin rashin tsaro da ke addabar ƙasar.

    Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne yayin wata walimar buɗe baki da ya shirya wa sanatoci a fadar shugaban ƙasa, inda ya ce "lokaci ya yi da za a bai wa jihohi ƙarin iko wajen kula da tsaron yankunansu."

    Ya ce "kafa ‘yan sandan jihohi zai taimaka wajen daƙile ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane, da hare-haren ‘yan bindiga, tare da ƙarfafa tattara bayanan sirri da kuma saurin mayar da martani idan barazana ta taso a cikin al’umma."

    Tinubu ya jaddada cewa tsarin rarraba ikon ‘yan sanda zai taimaka wajen haɗa kai tsakanin hukumomin tsaro na tarayya da na jihohi, tare da inganta yadda ake gudanar da ayyukan tsaro bisa sahihan bayanai.

    Ya kuma ce duk da kalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnati na da ƙudurin ganin an samar da mafita mai dorewa.

    A nasa bangaren, shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa sun ƙara yawan kuɗaɗen shiga ga jihohi, abin da ya ce zai taimaka wajen samar da muhimman ababen more rayuwa da bunkasa ci gaba a fadin ƙasar.

  6. Yau za a tantance yiwuwar cimma yarjejeniyar nukiliya tsakanin Amurka da Iran

    A yau ne za a gudanar da zagaye na uku na tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran a Geneva kan shirin makamin nukiliyar Tehran.

    Tattaunawar za ta tantance ko za a iya cimma wata yarjejeniya, inda Iran za ta iya haƙura da wasu daga cikin buƙatunta kan shirinta na nukiliya, ciki har da wasu ɓangarorin shirinta na Uranium.

    Ana kallon wannan tattaunawar da matukar muhimmanci, musamman yayin da Amurka ke ƙara karfin dakarunta a Gabas ta Tsakiya, mafi yawa tun bayan mamayar da ta kai wa Iraƙi a shekarar 2003.

    Iran itama ta ƙara karfafa shirinta domin tunkarar duk wani hari da ka iya zuwa.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan batun nukiliya, amma ya jaddada cewa yadda Iran ke dagewa kan cire batun makamai masu linzami shi ne babban ƙalubale a tattaunawar.

  7. Shin za a ci gaba da tsare El-Rufai har watan Afrilu, me doka ta ce?

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya shafe sama da kwana 10 a hannun hukumomin Najeriya.

    A ranar 16 ga watan Fabarairu ne El-Rufai, bisa raɗin kansa ya je ofishin hukumar yaƙi da rashawa da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC), domin amsa gayyatar da hukumar ta yi masa.

    Tun a farko hukumar EFCC ta tsare shi har zuwa daren Laraba 18 ga watan Fabrairu kafin daga baya aka miƙa shi hannun hukumar yaƙi da almundahana da dukiyar al'umma ta Najeriya (ICPC), inda tun daga wancan lokaci har yanzu ba a ƙara jin ɗuriyarsa ba.

    Ko a ranar Laraba da hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya DSS ta gurfanar da tsohon gwamnan a kotu, ba a ga Malam El-Rufain ba, kasancewar hukumar ICPC ba ta kai shi kotun ba.

    A ranar Laraba babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage ci gaba da sauraron karar da hukumar tsaron ta DSS ta shigar da El-Rufai game da zargin satar sauraron wayar mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu.

  8. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.