Fararen hula na shan baƙar wahala a birnin El Fashe na Sudan - MDD

Asalin hoton, Mohamed Zakaria/BBC
MDD ta ce ta ganewa idonta yadda farar hula ke tagayyare cikin bakar yunwa da tashin hankali a ziyarar farko da ta kai birnin El Fasher na Sudan tun bayan karbe ikon shi daga hannun 'yan tawayen RSF a watan Oktoba.
Wakiliyar BBC ta ce a ranar Juma'a ne karamar tawagar hukumar jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta kai ziyarar El Fasher, ta farko cikin kusan shekara 2, tun bayan kawanyar da 'yan tawayen RSF suka yi wa birnin.
Daraktar tsare-tsare na ayyukan jin kai na Majalisar Denise Brown, ta bayyana abin da suka gani da ainahin inda aka aikata mugun laifi, kuma kwararru kan kare hakkin dan adam za su gudanar da binke kan hakan, ya yin da ofishinta zai maida hankali kan kai agaji.

















