Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Najeriya ta kai zagaye na biyu bayan cin Tunisiya 3-2

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku bayanai kan wasan Najeriya da Tunisia a gasar kofin nahiyar Afirka ta 2025 da ake yi a Moroko.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Nan muka kawo karshen shirin

    Da fatan za ku tara a wani shirin na sharhi da bayanai kai tsaye a gasar cin kofin Afirka.

    Sunana Mohammed Abdu nake ce muku asuba ta gari.

  2. Wasan karshe na rukuni na uku ranar Talata

  3. Wasannin da za a buga ranar Lahadi, Najeriya 3-2 Tunisiya

  4. Sakamakon wasannin da aka buga ranar Asabar, Najeriya 3-2 Tunisiya

  5. Yadda teburin rukuni na uku yake bayan wasa na bibiyu

  6. An tashi wasa Najeriya ta kai zagaye na biyu, Najeriya 3-2 Tunisiya

  7. Kaɗan ya rage Tunisia ta farke ƙwallon, Najeriya 3-2 Tunisiya

    Kyaftin ɗin Tunisiya ka bugowa ƙwallo ya sa kai amma ta yi faɗi - har yanzu Tunisiya sai kai matsi take gidan Najeriya.

    Yanzu dai Super Eagles ta koma tare gida, domin ta tsira da wannan makin ukun da yake da mahimmaci a wajenta.

  8. Tunisiya na kai kora ko ta farke ɗayan da ya rage, Najeriya 3-2 Tunisiya

    Lokaci ya cika na minti 90 an kuma yi karin minti bakwai daga nan a tashi wasan.

    Ko Najeriya za ta kai zagaye na biyu kai tsaye da maki shida ko raaaba maki za ta yi da Tunisia? Sai a cikin karin lokacin nan za a tantance.

  9. Tunisia ta zare na biyu ta hannun Abdi, Najeriya 3-2 Tunisiya

    Mai tsaron bayan Tunisia, Abdi shi ne ya taɓe ya buga ƙwallon ta kuma faɗa ragar Najeriya, wanda ya buga ƙwallon da karfi don kada a samu matsala.

  10. A karon farko a wasan an je duba VAR

    Ana zargin Osayi-Samuel ya taɓa ƙwallo da hannu, an kammala duba VAR an kuma bai wa Tunisiya bugun fenariti.

  11. Najeriya ta yi sauye-sauye, Najeriya 3-1 Tunisiya

    Moses Simon ya maye gurbin Frank Onyeka

    Sannan kuma Chidera Ejuke ya cnaji Akor Adams.

  12. Tunisiya ta yi canji, Najeriya 3-1 Tunisiya

    Ɗan wasan Tunisiya, Ismaël Gharbi ya maye gurbin Elias Achouri.

  13. Tunisiya ta zare ɗaya ta hannun Talbi, Najeriya 3-1 Tunisiya

    Montassar Talbi na Tunisiya ne ya sa kai ta faɗa raga daga bugun da Hannibal Mejbri ya yi masa.

  14. Lookman ya ci wa Najeriya na uku

    Ƙwallo aka bai wa Osimhen ya shiga da ita da'irar Tunisia daga nan ya bai wa Lookman shi kuma sai da ya tsaya ya kaɗa kafa daga baya ya buga da kafar hagu sai ta bugi jikin mai tsaron gida ta faɗa raga.

  15. Tunisiya ta yi canji, Najeriya 2-0 Tunisia

    Tunisia ta saka Sebastian Tounekti ya maye gurbin Mohamed Ben Romdhane saboda raunin da ya ji.

  16. An bayar da katin gargaɗi ga Ajayi na Najeriya, Najeriya 2-0 Tunisiya

    An bai wa ɗan wasan tawagar Najeriya, Semi Ajayi katin gargadi, sakamakon ketar da ya yi wa Hannibal Mejbri, kuma ta yi muni kam

  17. Nageriya ta kara na biyu a ragar Tunisiya, Najeriya 2-0 Tunisiya

    Kwana ce aka kwaso ta hannun Ademola Lookman ta wuce kowa ta je wajen ƙyaftin Wilfred Ndidi ya yi tsalle ya sa kai ta kuma faɗa raga.

  18. , Najeriya 1-0 Tunisiya

    Osimhen ya saka fuskar kariya ta roba da aka koma zagaye na biyu, bayan sun sha ruwa sun huta.

  19. An koma zagaye na biyu a karawar ta hamayya, Najeriya 1-0 Tunisiya

  20. Yadda ƴan kallo suka je ganin wasan Najeriya da Tunisiya