Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/07/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/07/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Usman Minjibir da Aisha Babangida

  1. Dole ne Tinubu ya kawo ƙarshen zubar da jini a Zamfara - Amnesty

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Asalin hoton, STATE HOUSE

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Ƙungiyar kare hakkin bila'adama ta Amnesty International ta ce ya zama "wajibi" shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tabbatar an kawo ƙarshen kashe-kashen mutane da ke faruwa a jihar ta Zamfara da ke arewa maso yammacin ƙasar.

    Amnesty ta faɗi hakan ne a wani martani da ta mayar bayan kisan da ƴan bindiga suka yi wa mutane aƙalla 38 da suke garkuwa da su kisan gilla a ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda da ke jihar ta Zamfara.

    Sanarwar da Amnesty ta fitar a shafinta na X, ta ce "babu wani yanki na Zamfara da ke cikin aminci tun daga shekarar 2018.

    "A cikin shekara biyu da suka gabata an kashe sama da mutum 273 da yin garkuwa da mutane 467," in ji sanarwar.

    "Hukumomin Najeriya na da nauyin da ya rataya a kansu bisa dokokin ƙasa da na duniya, na kare dukkanin al'umma ba tare da nuna bambanci ba," in ji sanarwar.

    Zamfara na daga cikin jihohin Najeriya waɗanda suka shafe tsawon shekaru suna fama da matsalar ƴan fashin daji masu kisa da garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

    A lokuta daban-daban hukumomin Najeriya sun yi iƙirarin kashe manyan jagorori ƴan bindiga da ke jihar, sai dai kashe-kashen na baya-bayan nan na nuna cewa akwai sauran rina a kaba.

    A tattaunawarsa da BBC, shugaban ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda, Manniru Haidara Ƙaura ya ce yawancin waɗanda aka kashen matasa ne.

    "Bayanin da muka samu shi ne sun yi musu yankan rago ne. Abin da ya faru shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa kuma aka harhaɗa aka ba su kamar yadda suka nema, inda kuma suka saki mutum 18 da suka haɗa da mata 17 da ƙaramin yaro guda ɗaya, a ranar Asabar,"in ji Haidara.

  2. Akwai yunwa ta gaske a Gaza - Trump

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaban Amurka Donald Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce "akwai yunwa ta gaske" a Gaza.

    Shugaban na Amurka ya faɗi hakan ne bayan Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu yanace kan cewa babu yunwa a yankin.

    Lokacin da aka tambaye shi ko ya yadda da abin da Netanyahu ya fada cewar "ƙarya ce tsagwaronta" idan aka ce Isra'ila na ta'azzara yunwa a Gaza, shugaban na Amurka ya ce: "Ban sani ba...amma yaran nan da ka gan su, suna cikin yunwa...wannan yunwa ce ta gaske."

    Lokacin da ya yi magana sa'ilin da ya gana da Firaiministan Birtaniya Keir Starmer, Trump ya ce: "Babu wanda ya yi abin a zo a gani a can. Gaba ɗaya wurin ya lalace...Na faɗa wa Isra'ila cewa ƙila ya kamata su sauya salo."

    Kalaman Trump na zuwa ne bayan shugaban hukumar kai agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce ana buƙatar abinci mai "ɗimbin yawa" domin magance halin yunwa da yankin ke ciki.

  3. Tinubu ya yi wa ƴanmatan Najeriya da suka lashe kofi ruwan miliyoyi

    Tawagar Super Falcons da suka lashe kofin mata na Afirka a ranar Asabar

    Asalin hoton, X/CAFonline

    Bayanan hoto, Tawagar Super Falcons da suka lashe kofin mata na Afirka a ranar Asabar

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bai wa ƴan wasan tawagar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar 24 - Super Falcons - tukwicin kuɗi dala 100,000 kowanne, kimanin naira miliyan 153.

    Haka nan ya bai wa kowa daga cikinsu kyautar gida mai ɗaki uku, yayin da ya bai wa tawagar masu horas da su kyautar dala 50,000.

    Tinubu ya sanar da hakan ne a yau Litinin sa'ilin da ya tarbi tawagar matan bayan nasarar da suka samu ta lashe kofin ƙwallon ƙafa na Afirka karo na 10.

    A ranar Asabar ne Super Falcons suka lallasa Atlas Lionesses na Morocco da ci uku da biyu a wasan ƙarshe na gasar cin kofin da Moroccon ta karbi baƙunci.

    Baya ga kyautar kuɗi da gida, Tinubu ya kuma karrama ƴan wasan da lambar girmamawa ta ƙasa ta OON.

    Haka nan kuma ƙungiyar gwamnonin Najeriya ta bai wa tawagar ta Super Falcons kyautar kudi naira miliyan 10.

    Bayanan bidiyo, Kalli yadda Super Falcons suka koma Abuja bayan lashe kofi

    A lokacin da yake jawabi, Tinubu ya ce: "Na karɓi wannan kofi a madadin ƴan Najeriya, kuma zan ce muku: mun gode da wannan ƙwazo, saboda haka na karrama ƴan wasan da masu horas da su 11 da lamabar girmamawa ta Officer of the Order of the Niger (OON).

    "Bugu da ƙari na bayar da umarnin a bai wa dukkanin ƴan wasa da masu horas da su gidaje masu ɗakuna uku-uku.

    "Haka nan kuma, akwai kyautar kudin naira kwatankwacin dala 100,000 ga kowace ƴar wasa 24 da kuma dala 50,000 ga tawagar masu horaswa."

  4. MDD ta yi Allah-wadai da harin ƴan bindiga a Gabashin DR Congo

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ya Allah-wadai da wani mummunan hari da 'yan bindiga masu alaƙa da ƙungiyar IS suka kai a gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo inda aka kashe akalla mutane 43.

    Mafi yawan waɗanda suka mutu mabiya addinin Kirista ne, ciki harda wasu mutane da ke cikin ibada a lokacin da dakarun Allied Democratic Forces (ADF) suka kai harin a daren Asabar.

    Ana kuma zargin cewa wasu mutane da dama an sace su a lokacin harin.

  5. Adadin mutanen da suka mutu a Gaza tun fara yaƙi ya kai 59,921

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar lafiyar Hamas a Gaza ta bayyana cewa mutane 100 sun mutu cikin sa’o’i 24 da suka gabata, lamarin da ya kai jimillar mutanen da suka mutu tun bayan fara yaƙin zuwa 59,921.

    Haka kuma, an ƙarin 382 ne suka jikkata, wanda hakan ya sa adadin waɗanda suka jikkata ya haura zuwa 145,233.

    Wannan sabon adadi na mace-mace ya zo ne bayan dakartar da kai hare-hare na sa'o'i 10 domin isar da kayan jin ƙai a Gaza da Isra'ila ta amince da daga ƙarfe 10:00 zuwa 20:00 na agogon gida.

    Tun a baya an sanar da cewa mutum 14 sun mutu sakamakon yunwa da rashin abinci mai gina jiki cikin sa’o’i 24 da suka wuce.

  6. Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta ba tare da ɓata lokaci ba kuma ba tare da wani sharaɗi ba” bayan kwana biyar na faɗa a kan iyakar ƙasashen biyu.

    Faɗar ta yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 33 tare da raba dubban mutane da muhallansu.

    “Wannan babban mataki ne na farko wajen rage rikici da dawo da zaman lafiya da tsaro,” in ji firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, yayin da yake sanar da dakatar da faɗa yana mai cewa an cimma matsaya cewa za a daina faɗa daga ƙarfe 12 na dare.

    A farko, Thailand ta ƙi amincewa da tayin shiga tsakani da Anwar ya bayar, sai dai ta amince daga bisani bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba za a cigaba da tattaunawar haraji ba har sai “an daina faɗa”.

    Tashin hankali a kan tsohuwar takaddamar kan iyaka ya ƙara ƙamari a watan Mayu bayan wani sojan Cambodia ya mutu a wata arangama.

    Daga bisani kuma Thailand ta sanya takunkumi ga 'yan ƙasa da yawon bude ido daga shiga Cambodia ta hanyar ƙasa, yayin da Cambodia ta haramta shigo da wasu kayayyaki daga Thailand.

    Lamarin ya ƙara ta’azzara a makon da ya gabata, bayan wani soja dan Thailand ya rasa ƙafarsa a fashewar bam.

  7. Yadda ƴanbindiga suka yi wa mutum 38 yankan rago a Zamfara

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi musu yankan rago, daga cikin mutum 56 da suka yi garkuwa da su sakamakon gaza biyan kuɗin fansa da ƴanbindigar suke nema.

    Mutanen da aka kashe ɗin sun kasance ƴan ƙauyen Banga da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar ƙauran Namoda da ke jihar Zamfara.

    Shugaban ƙaramar hukumar, Manniru Haidara Ƙaura wanda ya shaida wa BBC yadda al'amarin ya faru, ya ce yawancin waɗanda aka yi wa yankan ragon matasa ne.

  8. Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin gwamnatin jihar, ta fara yajin aikin gargaɗi na kwana uku saboda rage musu albashi ba tare da sanarwa ba.

    A wata sanarwa da shugabannin ƙungiyar, Dr Japhet Olugbogi da Dr Adekunle Akinade, suka fitar, sun ce gwamnatin jihar ta rage albashin likitoci a watan Yuli ba tare da wata shawara ko sanarwa ba, duk da halin matsin tattalin arziki da ake ciki.

    Ƙungiyar ta ce sun tattauna da gwamnati bayan hakan, kuma an kafa kwamiti don sasanta lamarin, amma duk da haka, an sake rage albashin a watan Yuli, wanda suka bayyana a matsayin rashin adalci da saɓawa doka.

    Likitocin sun ce "mafi girman albashin babban likita a Legas bai kai dala 1,100 ba, amma gwamnati ta zaɓi rage wannan kuɗin maimakon ƙarfafa gwiwarsu."

  9. Faransa da Saudiyya na jogorantar tattaunawar samar da ƙasashen Isra'ila da Falasɗinu

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Faransa da Saudiyya na jagorantar wani taron tattaunawa na kwanaki uku na MDD da nufin farfaɗo da fatan samar da ƙasashe biyu tsakanin Isra'ila da Falasdinu.

    Ga Faransa dai, wani yunƙuri ne na gina goyon bayan shugaba Emmanuel Macron na amincewa da ƙasar Falasɗinawa nan gaba a wannan shekarar.

    Gwamnatin Trump dai na adawa da matakin - kuma Amurka za ta ƙaurace wa taron na MDD.

    Macron na fatan matakinsa zai tursasa wa Isra'ila da ƙasashe irinsu Birtaniya su aminta, domin samar da zaman lafiyan aka kasa samu

  10. Ciwon hanta da hanyoyin kamuwa da shi

    ...

    Asalin hoton, bbc

    Yau ce ranar yaƙi da cutar ciwon hanta ta duniya, kuma hukumar lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce mutane da dama ne ke ɗauke da wannan cuta wadda a Turance ake kira Hepatitis, amma ba tare da sun sani ba.

    Alƙaluma sun nuna cewa, miliyoyin mutane ne cutar ta Hepatitis ke hallakawa a faɗin duniya.

    An dai ware wannan rana ne domin jawo hankali ga illar wannan cutar, da kuma hanyoyin da ya kamata a bi domin shawo kanta.

    Likitoci na shawartar al'umma da su rinƙa zuwa gwajin cutar domin ba kasafai take nuna alamu ba kafin ta yi tsanani.

  11. NIMC ta gargadi ƴan Najeriya kan bayar da bayanansu

    ...

    Asalin hoton, NIMC

    Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC) ta bayyana damuwarta kan yadda wasu ƴan ƙsar ke sayar da bayanansu, ciki har da lambar shaidar ɗan kasa (NIN), domin samun kuɗi.

    Wannan na zuwa ne bayan sanarwar da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta fitar cewa wasu mutasa na biyan mutane naira 1500 zuwa 2000 don karɓar bayanansu sannan su sayar da su ga wasu kamfanonin hada-hadar kuɗi a kan naira 5000.

    A wata sanarwa da shugaban sashen hulɗa da jama’a na hukumar, Dr. Kayode Adegoke ya fitar, sanarwar ta ce ba za ta ɗauki alhakin duk wani bayani da mutum ya bayar da kansa ko ta wani ba, musamman idan hakan ya kasance domin samun kuɗi ko riba.

    NIMC ta bayyana cewa wannan lamari yana da matuƙar haɗari ga tsaron ƙasa da kuma tsaron rayuwar masu NIN ɗin wanda dalilin hakan ne hukumart gargaɗi ƴan Najeriya da kada su dinga bayar da bayanansu ga kowanne mutum da ba ma'akacin hukumar ba.

    Hukumar ta NIMC ta sha jan kunnen al’umma a baya cewa kada su rika bayyana lambar NIN dinsu ga kowanne mutum sai da ga ma'aikacin NIMC ko kuma waɗanda hukumar ta amince da su

  12. 'Mutum 14 sun mutu cikin sa’o’i 24 sakamakon yunwa a Gaza'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta ce mutum 14 ne suka mutu cikin sa’o’i 24 da suka gabata sakamakon yunwa da rashin abinci mai gina jiki.

    Cikin waɗanda suka mutu akwai yara biyu.

    Ma’aikatar ta ce jimillar mutanen da suka mutu saboda yunwa yanzu sun kai 147 – ciki har da yara 88.

  13. Hotuna daga taron tattaunawar zaman lafiya tsakanin Thailand da Cambodia

    Shugabannin ƙasashen Thailand da Cambodia yanzu sun hallara yayin da ake gudanar da tattaunawar zaman lafiya a gidan firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, da ke Putrajaya – kimanin mintuna 30 daga babban birnin ƙasar, Kuala Lumpur.

    Jami’ai daga Amurka da China, waɗanda duka sun bayyana buƙatar ganin an rage tashin hankali, suma sun halarci taron.

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

  14. Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

    ...

    Asalin hoton, other

    Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na iya fuskantar katsewar wuta daga ranar Litinin, yayin da kamfanin rarraba wutar Lantarki na Najeriya (TCN) zai fara aikin gyare-gyaren a layin wuta na Omotosho zuwa wani yanki na Ikeja West.

    A cikin wata sanarwa, TCN ya bayyana cewa hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta Najeriya (NERC) da kuma Hukumar tsarin rarraba Wuta ta Ƙasa (NISO) ne suka amince da gyare-gyaren.

    “Gyaran zai haɗa da shimfiɗa wasu wayoyi na wutar a layin wutar lantarki na Omotosho/Ikeja wanda aka shirya farawa daga ranar 28 ga Yuli, 2025 zuwa 21 ga Agusta, 2025 daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma,” in ji sanarwar da shugabar hulɗa da Jama’a na TCN, Ndidi Mbah, ta fitar.

    Ta kara da cewa bayan kammala aiki a kowace rana, za a maido da wuta ta wannan layi, kuma sauran layukan zasu ci gaba da aiki domin tabbatar da cewa Legas na samun isasshen wuta.

    Haka kuma, kamfanonin rarraba wutar lantarki na Eko da Ikeja sun shaida wa abokan cinikayarsu cewa za a fuskanci “yawan katsewar wuta lokaci-lokaci” a lokacin aikin.

  15. Hotunan yadda hargitsi ya ɓarke a ƙarshen mako yayin raba agaji a Gaza

    Mun ji a baya daga shugaban agaji na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher, kan yadda ake fuskantar ƙalubale wajen shigar da agaji zuwa Gaza.

    Ga wasu hotuna daga yankin Gaza a ƙarshen mako da ke nuna yadda aka samu hargitsi yayin raba kayan agaji a Gaza.

    ...

    Asalin hoton, EPA

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

  16. Tarayyar Turai da Amurka sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabannin ƙasashen Turai sun yi maraba da yarjejeniyar kasuwanci da suka ƙulla da Amurka, wadda ta kawo karshen fargabar rikicin kasuwanci da aka shiga.

    Yarjejeniyar, da aka cimma bayan wata tattaunawa a Scotland tsakanin shugaba Trump da Ursula von der Leyen, an amince da harajin kashi 15 cikin dari kan kayayyakin Tarayyar Turai - rabin harajin da Mista Trump ya yi barazanar ƙaƙabawa kenan.

    EU ta kuma amince za ta ƙara zuba jari a fannin makamashin Amurka.

    Ba a san abin da Amurka za ta bayar ba a nata Ɓangaren, duk da cewa babu cikakken bayani game da yarjejeniyar

  17. Thailand da Cambodia za su tattauna matakan zaman lafiya yayin da rikicin iyaka ke tsananta

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shugabannin Thailand da Cambodia za su yi wata ganawa domin tattauna matakan zaman lafiya a Malaysia, yayin da rikicin kan iyakar ƙasashen ya shiga rana ta biyar.

    Taron na zuwa ne bayan shugaba Trump ya gargaɗi ƙasashen cewa zai dakatar da tattaunawa da su kan rage harajin da ya ƙaƙaba masu, idan har ba su daina faɗa da juna ba.

    Rikicin ya hallaka rayuka da dama tare da raba dubbai da gidajensu.

    Cambodia ta ce a shirye take ta amince da tsagaita wuta.

  18. Tsagaita wutar sa'a 10 a Gaza ta fara aiki domin shigar da kayan agaji

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Isra’ila ta fara aiwatar da sabon tsarin dakatar da hare-hare na sa'o'i 10 a kullum a wasu yankunan Gaza, domin ba da damar kai kayan agaji ga mutanen da ke cikin mawuyacin hali.

    Sojojin Isra’ila sun ce daga ƙarfe 10 na safe zuwa 8 na dare (agogon Gaza), za a dakatar da hare-hare a yankuna uku da suka haɗa da El-Mawasi da tsakiyar Deir al-Balah da arewacin birnin Gaza.

    Wannan zai bai wa Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙungiyoyi damar raba abinci da magunguna.

    A halin da ake ciki, babban jami'in bada agaji na Majalisar Dinkin Duniya ya ce rahotannin da suke samu na nuni da cewa an tara sama da tirela 100 ɗauke da kayan agaji da za a shigar da su Gaza, bayan sassaucin da Isra'ila ta yi.

    Matsin lambar ƙasashen duuniya ce dai ta sa Isra'ila bayar da damar shigar da kayan agajin a wasu yankunan tare da dakatar da kai hare-hare

    Sai dai, duk da wannan sassauci, rahotanni sun nuna cewa har yanzu ba a samu cikakken tsaro ba.

    A jiya, rohotanni sun tabbatar da wani hari da ya faru a yammacin birnin Gaza, inda ake cewa an dakatar da hare-hare tun sa’a guda kafin hakan.

    Sojojin Isra’ila sun ce ba su da masaniya kan harin da aka kai a wajen lokacin dakatar da farmaki.

  19. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Litinin.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.