Gwamnatin Najeriya ta rufe kwalejojin tarayya saboda matsalar tsaro
Gwamnatin Najeriya ta sanar da umarnin rufe makarantunta na sakandare na kwalejojin tarayya da ake kira da Unity Colleges.
A wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a ranar Juma'a wadda daraktan makarantun sakandare, Binta Abdulqadir ta sanya wa hannu a madadin ministan ilimi Tunji Alausa, gwamnatin ƙasar ta sanar a rufe kwalejojin guda 47 a faɗin Najeriya.
Sanarwar ta ce ma'aikatar ta ɗauki wannan matakin ne "saboda barazanar tsaro da ake fuskanta a wasu sassan ƙasar, da kuma yunƙurin daƙile aukuwa wata matsala," kamar yadda sanarwar ta nuna.
Sanarwar ta kuma umarci shugabannin makarantun su tabbatar an aiwatar da umarnin.