Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 17/12/2025.

Wanna shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 17/12/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Mene ne ƙarfin sojin Najeriya?

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Tun bayan ɗaukin gaggawa da sojojin saman Najeriya suka kai ƙasar Benin inda suka taimaka wajen daƙile yunƙurin juyin mulki da sojoji suka so yi, ƴan Najeriya da ma Afirka sanin irin karfin da Najeriya ke da shi idan aka kwatantan da sauran ƙasashen Sahel.

    Baya ga tura jiragen yaƙi, majalisar dokokin Najeriya ta kuma amince da buƙatar Bola Tinubu na aikewa da rundunar soji zuwa Benin ɗin domin wanzar da zaman lafiya.

    Ana cikin haka ne kuma sai hukumomin Burkina Faso suka riƙe wani jirgin sojin Najeriya ƙirar C-130 tare da mutane 11 da yake dauke da su.

    Ƙungiyar ƙasashen Sahel, wadda ta ƙunshi Jamhuriyar Nijar, Mali da Burkina Faso sun zargi jirgin na Najeriya da keta hurumi ta hanyar tsallake iyaka ba bisa ƙa'ida ba.

    Najeriya a nata ɓangaren ta ce jirgin yana kan hanyarsa ce ta zuwa ƙasar Portugal, inda ya samu tangardar na'ura, lamarin da ya tursasa masa yin saukar gaggawa a ƙasar ta Burkina Faso, kuma hukumomin sun ce an yi komai ne "a kan tsari."

  2. Dalili uku da suka sa Trump ya haramta wa wasu ƴan Najeriya da Nijar shiga Amurka

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    A daidai lokacin da ake ci gaba da tafka muhawara kan zargin ana cin zarafi ko kuma yi wa Kiristocin Najeriya kisan kiyashi, musamman a arewacin ƙasar, gwamnatin Amurka ta ɗauki matakin hana wasu ƴan Najeriyar shiga ƙasarta.

    Wata sanarwa da fadar gwamnatin Amurka ta fitar a ranar Talata ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da za a taƙaita wa mutanenta shiga Amurka.

    Ko waɗanne dalilai Amurkar ta dogara da su wajen taƙaita shigar ƴan Najeriya cikin ƙasarta?

    • Boko Haram: A sanarwar da gwamnatin Amurka ta fitar, ta ce masu tsattsauran ra'ayin addini kamar Boko Haram da tsagin ISWAP suna gudanar da hare-hare a wasu sassan Najeriya yadda suke so.
    • Zaman wuce wa'adin biza: Sanarwar ta ƙara da cewa akwai waɗanda suke shiga ƙasar da bizar ɗan ƙanƙanin lokaci, amma sai su ci gaba da zama bayan wa'adin ya ƙare. Ta ce masu na'ukan bizar B-1/B-2 kusan kashi 5.56 ne suke zaune a ƙasar duk da bizarsu ta ƙare, sannan masu na'ukan bizar F da M da J kusan kashi 11.90 ne suke zaune ba bisa ƙa'ida ba.
    • Matsalar tantancewa: A wani ɓangaren kuma, fadar gwamnati Amurka ta ce matsalolin tsaron, suna kawo tsaiko wajen tantance ƴan ƙasar, lamarin da bai rasa nasaba da gane baƙin haure da masu zuwa wani aikin daban. Karanta cikakken labarin a nan
  3. Wane ne Injiniya Saidu Aliyu da zai maye gurbin Farouk Ahmed?

    ..

    Asalin hoton, LinkedIn

    Jim kaɗan bayan sanar da murabus da Ahmed Farouk ya yi daga shugabancin hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutumin da zai gaje shi.

    A wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya ce shugaba Tinubu ya nemi majalisar dattawa da ta amince da naɗin da ya yi wa Injiniya Sa'idu Aliyu Mohammed a matsayin sabon shugaban NMDPRA.

  4. Ahmed Musa ya yi ritaya daga buga wa Najeriya wasa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan Najeriya wanda a tarihi ya fi kowane ɗan wasan ƙasar yawan cin ƙwallaye a Gasar cin Kofin Duniya, Ahmed Musa ya sanar da yin ritaya daga buga wa ƙasar wasa.

    Musa, wanda tarihi zai daɗe yana tuna shi sanadiyyar gudumawar da ya bai wa ƙasar ya ce: "na yanke shawarar daina buga wa ƙasata wasa, wanda ya kawo ƙarshen shekara 15 da na yi tare da ƙungiyar Super Eagles," kamar yadda ya bayyana a shafinsa na sada zumunta.

    Ahmed Musa ya buga wa Najeriya wasanni 111 ya bayyana taka wa Najeriya wasa a matsayin "abin da ya fi masa komai".

    Ya buga wa Najeriya wasanni a matakin ƴan ƙasa da shekara 20 da ƴan ƙasa da shekara 23 da kuma babbar tawagar Najeriya ta Super Eagles.

    "Zama mutumin da ya fi kowa buga wa Najeriya wasa a tarihin ƙwallon ƙafa babbar karramawa ce gare ni," in ji Musa a cikin sanarwar da ya fitar.

  5. Labarai da dumi-dumi, Shugaban hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed ya yi murabus

    ..

    Asalin hoton, NMDPRA

    Shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, Ahmed Farouk.ya ajiye aikinsa.

    Wata sanarwa daga fadar shugaban Najeriya ta ce tuni shugaba Tinubu ya aike da sunan mutumin da zai gaji Farouk Ahmed.

    Sanarwar ta ce shugaba Bola Tinubu ya nemi majalisar dattawa da ta amince da naɗin Engineer Saidu Aliyu Mohammed a matsayin shugaban hukumar ta NMDPRA.

    Shi ma shugaban hukumar NUPRC, Gbenga Komolafe ya sauka daga muƙaminsa, inda shi ma fadar shugaban ƙasar ta aike da sunan mutumin da zai gaje shi.

    Wannan dai na zuwa ne kwana uku bayan da shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote, Aliko Dangote ya yi zargin cewa Farouk Ahmed na biya wa ƴaƴansa guda huɗu kuɗin makaranta a Switzerland da suka kai dala miliya biyar.

    Tuni dai hukumar yaƙi da almundahana ta Najeriya ICPC ta ce za ta yi bincike kan zargin da shugaban rukunin kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya yi wa shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, Ahmed Farouk.

  6. Babu barazanar da muke yi wa ƙasashen Turai - Putin

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Rasha, Vladimir Putin ya ƙaryata zargin da ke nuna cewa Rasha na yi wa ƙasashen Turai wata barazana, lamarin da ya bayyana da ƙazon-kurege.

    Ya yi wannan martanin ne bayan ƴan siyasa da shugabannin sojoji a Turai sun yi gargaɗin cewa Rasha na iya yaƙar ƙasashen yamma gaba daya.

    Shugaban haɗakar tsaro ta NATO Mark Rutte ya ce matuƙar Rasha ta samu nasarar cika burin da take da shi a Ukraine, za ta yi yunƙurin faɗaɗa farmakinta zuwa wasu yankunan na turai.

    Putin dai ya ce ba bu gaskiya a batun.

  7. ..

    Asalin hoton, BBC COLLAGE

    Babban batun da ya fi jan hankalin ƴan Najeriya a makon nan shi ne musayar yawu tsakanin shugaban kamfanonin Dangote, Aliko Dangote da shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, Ahmed Farouk.

    Al'amarin ya yi amon da har ta kai ga hukumar yaƙi da almundahana ta Najeriya ICPC, ta ce za ta yi bincike.

    Bugu da kari, rikicin ya raba kan ƴan Najeriya biyu, inda wani ɓangare ke ganin abin da Ɗangote ya yi daidai ne sannan ɗaya ɓangaren yake kallon bai kamata ba inda suke goyon bayan Farouk Ahmed.

    BBC ta yi nazari da bibiyar mahawar da al'amarin ya janyo inda ta fito da wasu abubuwa guda 5 da suka fito fili a sa-in-sar.

  8. Ruwan sama da iska na ta'azzara matsalolin da yara ke fuskanta Gaza - UNICEF

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadin cewa ruwan sama da iska mai ƙarfi a Gaza na ƙara tsananin yanayi a yankin.

    Ya ce dubun dubatan yaran da ke rayuwa a matsattsun tentuna na fuskantar hatsarin kamuwa da cutuka.

    Iyaye na fafutukar yadda za su kare yara da ruwa.

    Hukumar Majalisar Dinkin duniya ta ce kusan mutane miliyan 'daya na rayuwa cikin tentunan da basa iya kare su daga ruwan sama ko tsanin sanyi, hukumar ta kuma neni 'karin kayan agaji.

  9. Gwamnan Sokoto ya gabatar da kasafin sama da naira biliyan 750

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu

    Asalin hoton, Gwamnatin Jihar Sokoto

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya gabatar da kasafin kuɗin shekara ta 2026 ga majalisar dokokin jihar, wanda ya ƙunshi kuɗi naira biliyan 758,700,526,537.89.

    Gwamnan ya yi wa kasafin kuɗin taken 'kasafin faɗaɗa walwala da tattalin arziƙi."

    Bayanin da gwamnan ya yi ya nuna cewa za a kashe naira biliyan 551,493,592,537.89 kan manyan ayyuka, yayin da ayyukan yau da kullum za su laƙume kuɗi naira biliyan 207,206,934,434.43.

    Ɓangaren lafiya na jihar na daga cikin waɗanda suka samu kaso mafi tsoka inda zai laƙume kudi sama da naira biliyan 122.

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu

    Asalin hoton, Gwamnatin Jihar Sokoto

    Daga cikin ayyukan da za a aiwatar sun haɗa da kammala aikin gina asibitin koyarwa na jami'ar jihar Sokoto a unguwar Ƙasarawa da wasu manyan asibitocin.

    Haka nan gwamnatin jihar za ta sayi motocin daukar marasa lafiya guda 21 domin rabawa a manyan asibitocin jihar.

    Ɓangaren ilimi ya samu kuɗi sama da naira biliyan 115, ɓangaren ayyuka da sufuri zai lashe sama da naira biliyan 109.

    Ɓangaren tsaro ya samu kuɗi sama da naira biliyan 45, wanda za a kashe wajen sayen kayan tallafa wa harkokin tsaro, waɗanda suka hada da motoci da baburan sintiri na jami'an tsaro.

    An kuma ware sama da naira biliyan 33 a harkar tallafin agaji.

  10. An tuhumi ɗan Indiyan da ya kashe mutum 51 a Bondi da laifuka 59

    ...

    Asalin hoton, Saeed KHAN / AFP via Getty Images

    Ƴansanda a Australia sun tuhumi ɗan Indiyan da ake zargi da harbe mutum 51 a Bondi da laifuka 59 da suka haɗa da kisan kai da kuma ayyukan ta'addanci.

    An sanarwa Naveed Akram tuhumar da ake masa yayin da ya farfado daga dogon suma a asibiti.

    An shaida wa BBC cewar a ɗage shari'ar zuwa watan Afirilun ba'di.

    Mahaifinsa Sajid Akram ya rasa ransa sakamakon harbin da ƴansanda suka yi masa yayin harin lokacin da Yahudawa ke bukin Hajnukkah.

    Gwamatin Philliphiness ta yi watsi da zargin cewa mutanen biyu sun samu horon soji a ƙasar.

  11. An tsare ma’aikatan lafiya da dama a babban birnin Darfur ta Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban hukumar lafiya ta duniya WHO, Dr. Tedros Ghebreyesus, ya bayyana damuwa kan rahotannin da ke cewa an tsare ma’aikatan lafiya da dama da ƙarfi a yankin kudu maso yammacin Sudan.

    Wannan na zuwa ne bayan bayanan da cibiyar likitocin Sudan ta fitar, inda ta ce ma’aikatan lafiyar na daga cikin dubban fararen hula da ake tsare da su a birnin Nyala, babban birnin jihar Darfur ta Kudu.

    A cewar Tedros, aƙalla ma’aikatan lafiya 70 ne ke cikin sama da fararen hula 5,000 da ake zargin ana tsare da su ba tare da izini ba a Nyala, wanda shi ne hedikwatar dakarun RSF.

    Rahotanni sun nuna cewa ana tsare da mutanen ne a wurare masu cunkoso da rashin tsafta, lamarin da ya haddasa yaɗuwar cututtuka.

    Shugaban na WHO ya ce hukumar na ci gaba da tattara ƙarin bayanai kan lamarin, amma ya bayyana cewa tsananin rashin tsaro da ke addabar yankin na kara dagula fahimtar ainihin halin da ake ciki.

    Ya yi kira da a gaggauta sakin ma’aikatan lafiyar ba tare da sharaɗi ba, tare da tabbatar da tsaron rayuwarsu.

    Tun daga shekarar 2023, dakarun RSF da sojojin Sudan ke fafatawa a wani mummunan yaƙi da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da tilasta wa miliyoyi barin muhallansu.

  12. Ana zargin gwamnatin Tinubu da sauya dokar haraji bayan amincewar majalisa

    Tinubu

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

    Ɗan majalisar wakilan Najeriya daga jihar Sokoto Abdulsammad Dasuki ya ja hankalin majalisar kan abin da ya bayyana da bambance-bambance da ya yi zargin ya gano a tsakanin ƙudurin dokar haraji da majalisar ta amince da shi, da kuma wanda aka aka sanya wa hannu ta zama dokar da za a yi amfani da ita.

    Dasuki ya ce an take masa haƙƙinsa na ɗan majalisa, inda ya nanata cewa abin da aka takardun dokar da aka fitar sun bambanta da abin ‘yan majalisar suka tattauna, sannan suka kaɗa ƙuri'ar amincewa.

    Ya ce ya yi wannan ƙorafin a ƙarƙahin damar da yake da ita dta haƙƙin ƴan majalisa da kundin dokokin majalisar ta tanada.

    Ya ƙara da cewa bayan amincewa da dokokin haraji ne ya ɗauki kwana uku yana nazarinsu, inda ya ce a hakan ne ya gano akwai bambanci da wanda majalisa ta amince ta ita.

    “Ina nan lokacin da aka yi tattaunawar, kuma na kaɗa ƙuri’a a kan lamarin, amma yanzu ina ganin wani abu daban da abin da muka amince da shi."

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da ƙudororin yi wa harajin garambawul, lamarin da ya tayar da ƙura kafin ƴan majalia suka amince.

    A sabuwar shekarar da za a shiga ne dai sababbin dokokin harajin za su fara aiki.

  13. Mutum huɗu sun tsira bayan wani jirgi ya yi hatsari a filin jirgin Owerri

    ...

    Asalin hoton, NTA

    Mutum hudu sun tsira daga hatsarin jirgin sama da ya faru da yammacin Talata a filin jirgin sama na Sam Mbakwe da ke Owerri, jihar Imo.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktar hulɗa da Jama’a na hukumar tabbatar da aminci a ɓangaren sufuri ta Najeriya (NSIB), Bimbo Oladeji ta fitar.

    Sanarwar ta ce hatsarin ya faru ne sa'ilin da yake ƙoƙarin sauka a filin jirgin.

    Jirgin na kan hanya ne daga Kaduna zuwa Fatakwal, inda matukan jirgin suka bayyana cewa an samu tangardar na'ura dalilin da ya saka suka karkata zuwa Owerri.

    Jami’an tsaro da na kai ɗaukin gaggawa a filin jirgin sun gaggauta zuwa wurin, inda suka ceto ɗaukacin fasinjojin jirgin.

    Ba a samu tashin wuta ba bayan hatsarin, kuma hakan bai kawo cikas ga harkokin sauka da tashin jirage ba a filin.

  14. Majalisa ta buƙaci gwamnati ta ɗauki mataki kan tsadar kayan noma

    ...

    Asalin hoton, Nigeria Senate

    Majalisar dattawan Najeriya ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta ɗauki matakin gaggawa don rage wa manoman ƙasar asarar da suke yi sakamakon faduwar farashin amfanin gona, inda ta yi gargaɗin cewa idan ba a shawo kan lamarin ba, zai iya yin barazana ga rayuwar miliyoyi da kuma wadatar abinci a kƙasar.

    Kiran ya biyo bayan amincewa da wani ƙudirin da Sanata Mohammed Danjuma Goje mai wakiltar Gombe ta tsakiya ya gabatar,wanda ya nuna rashin daidaiton da ake samu tsakanin faɗuwar farashin amfanin gona da kuma tsadar kayan noma a kasar yanzu.

    Bayan tashi daga zaman majalisar, BBC ta tambayi Sanata Goje abin da ya ja hankalinsa na gabatar da kudurin, saim ya ce;

    "Damuwa ne nake gani ya samu dukkan manoma a Najeriya gaba ɗaya musamman ƴan arewa, amfanin gona farashinsa ya dawo ƙasa amma kuma abubuwan da ake amfani da su wajen noma musamman taki da maganin feshi, farsashinsu bai ragu ba ko kaɗan."

    "Toh sai ta kai ga yanzu a bana, sai ka ga abin da manomi ya kashe yayi noma da kyar ya sami rabin wannan kudin idan ya kai amfanin gonansa kasuwa." in ji shi.

    "Sai na ga idan wannan abu ya ci gaba, za a wayi gari a ga jama'a ko dai su bar noma ko kuma abin da suke da shi ya ƙare gaba ɗaya."

    "Wannan ne ya saka na gabatar da ƙudirin" in ji Sanatan.

    Sanatan ya ce yana matuƙar farin ciki da saukar farashin kayan abinci ya sauka amma yana kira da a duba al'amarin manoma saboda rayuwarsu kuma ganin sun fi kowa yawa a ƙasar.

    Sanatan ya ƙara da cewa abin da yake so gwamnati ta yi shine ta ɗauki mataki kan yadda za a yi a samar da taki da maganin feshi dayawa kuma farashinsu ya yi ƙasa su ma kamar yadda farashin amfanin gona ya yi ƙasa.

  15. An kama ƴan Kenya bakwai a Afrika ta Kudu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Afirka ta Kudu sun kama ƴan Kenya 7 da ake zargin suna aiki ba bisa ƙa'ida ba a wani cibiyar da ke shirin karɓar ƴan gudun hijira na Amurka.

    Hukumar harkokin cikin gida ta ce waɗannan ma’aikatan sun shiga ƙasar ne da biza ta yawon shakatawa, wadda ba ta ba su damar yin aiki ba.

    Hukumar ta bayyana cewa an yi wannan bincike ne bisa bayanan sirri da aka samu cewa wasu ƴan ƙasashen waje suna aiki ba bisa ƙa'ida ba a cibiyar.

    A baya, an ƙi ba da biza ga ƴan Kenya saboda dalili makamancin wannan.

    Hukumomin sun ce za a kori waɗanda aka kama daga ƙasar kuma ba za su iya dawowa ba tsawon shekaru biyar.

  16. Ina maraba da ƙorafin da Dangote ya kai ICPC - Shugaban NMDPRA

    ...

    Asalin hoton, NMDPRA

    Shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da dufurin Man Fetur a Najeriya (NMDPRA), Farouk Ahmed, ya ce ƙarar da shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya kai shi gaban hukumomi inda yake zarginsa da cin hanci da almundahana wata dama ce da zai yi amfani da ita wajen wanke kansa daga duk wani zargi da ake yi masa.

    A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, Farouk Ahmed ya ce yana maraba da duk wata bincike ta hukuma, yana mai jaddada cewa hakan zai ba da damar a duba al’amuran cikin adalci da tsantseni domin a fayyace gaskiya.

    Ya ƙara da cewa ba zai tsaya yana ce-ce-ku-ce a bainar jama’a da Dangote ba, duk da zarge-zargen da ake yi masa, yana mai cewa hanya mafi dacewa ita ce bin tsarin doka da binciken hukuma.

    Shugaban na NMDPRA ya kuma jaddada cewa hukumar da yake jagoranta tana gudanar da ayyukanta bisa doka da ƙa’ida, tare da himmar tabbatar da gaskiya da adalci da kuma inganta tsarin kula da harkokin man fetur a Najeriya.

    A jiya Talata ne dai hukumar yaƙi da almundahana ta Najeriya ICPC ta ce za ta yi bincike kan zargin da Aliko Dangote ya yi wa Ahmed Farouk ɗin.

  17. Amurka ta haramta wa ƴan Najeriya da wasu ƙasashe shiga ƙasar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Shugaba Donald Trump ta sanar da sanya sabbin takunkuman hana shiga ƙasar, inda matakin ya shafi wasu ƙasashe ciki har da Najeriya saboda matsalar tsaro.

    Takunkumin ya haɗa da haramta shigar ‘yan ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar da Sudan ta Kudu, tare da mutanen da ke riƙe da takardun hukumomin Falasɗinawa.

    Fadar White House ta ce an ɗauki matakin ne domin kare tsaron ƙasar da kuma tabbatar da kariya ga al’ummar Amurka.

    Haka kuma, gwamnatin ta sanar da ƙwarya-ƙwaryar dakatar da tafiye-tafiye daga ƙasashe 15 ciki har da Najeriya, inda ta danganta matakin da barazanar tsaro da ayyukan ƙungiyar Boko Haram.

    Ƙasashen Laos da Saliyo, waɗanda a baya aka sanya musu ƙwarya-ƙwaryar takunkumi, yanzu an tsaurara musu matakin inda aka dakatar da shigar ‘yan ƙasashensu gaba ɗaya.

    Sabon takunkumin zai fara aiki ne daga watan Janairun 2026.

  18. NLC za ta gudanar da zanga-zanga kan matsalar tsaro a Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Facebook/Nigeria Labour Congress

    Ƙungiyar ƙwadado ta NLC a Najeriya, ta ce za ta gudanar da zanga-zangar lumana ta gama-gari, a fadin ƙasar saboda abin da ta kira ƙara tabarbarewar lamuran tsaro a ƙasar.

    NLC ɗin ta ce ta na son ganin gwamnati ta ƙara ɗaukar matakan tsaro, domin dakile wannan lamarin na tsaro a ƙasar baki ɗaya .

    Comrade Nasiru Kabiru, shi ne sakataran tsare-tsare na ƙungiyar ta NLC, ya shaida wa BBC cewa za su yi zanga-zangar ce saboda nuna bacin ransu akan yadda ɓangaren tsaro ya taɓarɓare.

    Ya ce," Idan kaje arewacin Najeriya tun daga jihohi Borno da Yobe da Zamfara da Sokoto da Kebbi, dukka dai yawancin waɗannan wurare na fama matsalar tsaro, haka idan kaje kudancin Najeriya ma haka lamarin ya ke."

  19. Za mu binciki shugaban NMDPRA kan ƙorafin Dangote - ICPC

    ...

    Asalin hoton, Getty Images/NMDPRA website

    Hukumar yaƙi da almundahana ta Najeriya ICPC ta ce za ta yi bincike kan zargin da shugaban rukunin kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya yi wa shugaban hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, Ahmed Farouk.

    Dangote ya mika ƙorafi ga hukumar ICPC a ranar Talata, inda ya zargi Farouk da cin hanci da rashawa da almundahanar kuɗaɗen gwamnati.

    Bayan sa’o’i kaɗan da shigar da ƙorafin, ICPC ta tabbatar da karɓarsa tare da bayyana aniyarta ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

    A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, John Odey, ya fitar a shafukan sada zumunta na ICPC, ya ce "Hukumar ta karɓi ƙorafin Dangote a hukumance a ranar Talata 16 ga Disamba, 2025, ta hannun lauyansa."

    A cikin ƙorafin, "Dangote ya zargi Farouk da kashe sama da dala miliyan 7 wajen biyan kuɗin karatun ’ya’yansa huɗu a makarantu a ƙasar Switzerland na tsawon shekaru shida, ba tare da bayyana sahihiyar hanyar samun kuɗin ba.

    Korafin ya ce Farouk ya yi amfani da muƙaminsa a NMDPRA wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati domin amfanin kansa, lamarin da ya janyo asara ga ’yan Najeriya.

    A nasa martanin, shugaban hukumar NMDPRA, Ahmed Farouk, ya ce yana maraba da binciken da hukumar ICPC za ta gudanarwa a kansa.

    Ya ce ya yi imanin cewa binciken zai ba da dama a duba lamarin cikin adalci da natsuwa, tare da fayyace gaskiyar al’amura domin wanke sunansa.

    Ahmed Farouk ya ƙara da cewa ba zai yi musayar zarge-zarge a bainar jama'a ba yana mai cewa zai bari binciken hukuma ya yi aikinsa yadda ya kamata.

  20. Trump ya dakatar da tankokin dakon mai shiga ko fita daga Venezuela

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ya bayar da umarnin a dakatar da dukkan tankokin dakon mai daga shiga ko fita daga Venezuela, matakin da zai kara matsawa gwamnatin shugabanbin Nicolas Maduro lamba.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya ce sun ƙara yawan sojojin Amurka, a kusa da Venezeula.

    Trump ya ce gwamnatin Maduro na ɗaukar nauyin ayyukan da suka shafi safarar ƙwayoyi da ta'addanci da safarar mutane da kisa da kuma satar mutane daga filyen man da ta sace.

    Kalaman nasa na zuwa ne kwanaki bayan da dakarun Amurka suka kƙwace wata motar dakon mai a yankin Karebiya tare da sanyawa wasu motocin shida takunkumi wani yunkuri da ya ce zai shafi hanyar kudin shigar kasar.

    Tuni dai gwamnatin Venezuela ta yi alawadai da matakin Trump din tana mai cewa ya take hakkin kasuwanci.