Ƙasashen Sahel sun ƙaddamar da tutar ƙawance

Asalin hoton, Burkina Faso Presidency
Gamayyar ƙasashen Sahel da suka haɗa da Mali da Burkina Faso da Nijar sun ƙaddamar da tutar ƙawancen ƙasashen a birnin Bamako na Mali.
Wannan matakin ya biyo bayan amincewar da shugabannin ƙasashen ƙungiyar suka yi a ranar 22 ga watan Fabrairu.
An gabatar da tutar ce a wajen wani taro na ministocin ƙungiyar da aka kammala a yau Lahadi 23 ga wannan wata da muke cikin.
Ministocin na AES ne suka ƙaddamar da tutar mai launin kore da kuma tambarin ƙungiyar a tsakiyarta.
















