Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/07/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/07/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Kotun MDD ta ce ƙasashe na iya kai juna ƙara kan sauyin yanayi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani muhimmin hukunci da wata babbar kotu ta Majalisar Dinkin Duniya ta yanke, ya share fagen shigar da ƙarar da ƙasashe za su iya yi kan juna bisa batutuwan da suka shafi sauyin yanayi.

    Sai dai mai shari'a a kotun duniyar da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands a ranar Larabar da ta gabata ya ce sanin wanda ya haddasa wani ɓangare na sauyin yanayi zai iya zama da wahala.

    Ana yi wa hukuncin kallon nasara ce ga ƙasashen da ke fama da matsalar sauyin yanayi, waɗanda suka zo kotu bayan da suka ji takaicin rashin samun ci gaba a duniya wajen tunkarar matsalar.

    Waɗansu ɗaliban shari'a ne daga kasashen Pacific masu ƙaranmin ƙarfi ne suka shigar da karar da ba a taba ganin irin ta ba a kotun duniyar (ICJ) a shekarar 2019.

    Ana yi wa ICJ kallon kotun ƙoli a duniya kuma tana da hurumin yanke hukunci kan al'amuran da suka shafi bangarori daban-daban na duniya. Lauyoyi sun shaida wa BBC cewa za a iya amfani da hukuncin nan da mako mai zuwa.

  2. 'Mutane na sayar da zinare domin su iya sayen fulawa a Gaza'

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Wata mata a arewacin Gaza ta ce mutane na sayar da zinari domin su samu kuɗin sayen fulawa a Gaza.

    Hanaa Almadhoun mai shekara 40, ta ce galibin kasuwanni ba su da abinci ko kuma kayan masarufi, kuma a inda aka same su, sukan kasance da tsadar gaske.

    "Fulawa, wanda shi ne tushen akasarin abincin mu, idan an same shi, yana da tsada domin yana da wuyar samu," in ji ta, ta ƙara da cewa mutane sun sayar da "zinarinsu da kayan sa wa" don samun kuɗin sayen kayan abinci.

    Mahaifiyar ƴaƴa uku ta ce "kowace sabuwar rana tana zuwa da sabon ƙalubale" yayin da mutane ke fita "don neman abun da za su ci".

    Ta ƙara da cewa "Da idona, na ga yara sun yi ta gararamba a cikin bola domin neman abinci." Ta na mai cewa "Babu audugar mata, babu ruwan wanka, babu dakunan wanka masu tsafta" in ji ta.

    Hanaa ta ce mutanen Gaza sun yi ƙoƙarin nemo wani abin da zai maye masu gurbin fulawa amma har yanzu lamarin ya ci tura.

  3. An tattauna batun tsagaita wuta tsakanin Rasha da Ukraine

    Putin & Zelensky

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    An kawo ƙarshen tattaunawar da aka yi na baya bayan nan tsakanin Rasha da Ukraine a Istanbul ba tare da an fitar da wata muhimminiyar sanarwa ba.

    Ɓangarorin biyu dai sun ce sun amince da yin aiki tare wurin kara musayar fursunoni na sojoji da na farar hula.

    Masu shiga tsakani na Ukraine sun ce babu wata yarjejeniya da aka cimma a tattaunawar tsakanin ƙasashen biyu amma Kyiv a shirye ta ke ta tsagaita wuta a yanzu.

    Fadar Kremlin ta sha yin watsi da fatan samun gagarumin ci gaba, tana mai cewa bambancin da ke tsakanin ɓangarorin biyu suna da yawa don haka zai yi wuya a iya cimma yarjejeniyar zaman lafiya.

  4. 'Ba kowace irin yarjejeniya Canada za ta amince da ita ba - Carney

    MArk Carney

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Canada Mark Carney ya ce ƙasarsa "ba za ta amince da wata mummunar yarjejeniya ba" a yunƙurinta na cimma yarjejeniyar kasuwanci da Amurka, yayin da wa'adin ranar 1 ga watan Agusta ke gabatowa lokacin da sabbin harajin shugaban Amurka Donald Trump za su fara aiki.

    "Manufarmu ba ita ce cimma matsaya ko ta halin ƙaƙa ba," in ji Carney ga manema labarai a Ontario.

    "Muna nemen cimma yarjejeniyar da za ta kasance mafi amfani ga mutanen Kanada."

    Masu shigar da kaya Amurka daga Kanada za su fuskanci harajin kashi 35% idan ba a cimma yarjejeniya ba kafin cikar wa'adin.

    Makwabtan na cikin manyan abokan cinikin juna, amma sun kasance cikin takun-saka bayan da Trump ya koma fadar White House a farkon wannan shekara ya kuma ƙaddamar da wani shiri na ƙaƙaba haraji kan ƙasashen duniya.

    Tuni Trump ya sanya harajin gama-gari na kashi 25 cikin 100 kan shigo da kayayyaki daga kasar Canada, da kuma harajin kashi 50% kan kayayyakin sanholo da ƙaraffa da ake shigo da su daga ƙasar ,

    Da yake magana kan batun kasuwancin, Carney ya ce zai yi nazarin ɗaukar matakin kare kamfanonin sanholo da katako, biyu daga cikin manyan masana'antu na ƙasar, yana mai nuni da yiwuwar ɗaukar wasu matakan kariya a duk lokacin da cikakken tsarin harajin Amurka ya fara aiki.

  5. Gwamnatin Jihar Sokoto ta bayar da kwangilar gyaran cibiyoyin lafiya 244

    Ahmed Aliyu

    Asalin hoton, Govt House Sokoto

    Gwamnatin jihar Sokoto ta bayar da kwangilar gyaran dukkan cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 244 dake jihar.

    Gwamna Ahmed Aliyu ya sanar da hakan ne a taron ƙaddamar da shirin kariya daga kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro na shekarar 2025 da aka gudanar a garin Achida da ke ƙaramar hukumar Wurno ta jihar.

    Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Idris Mohammed Gobir, ya yi kira ga ɗaukacin shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki da iyaye da su bai wa wannan shirin haɗin kai ta hanyar wayar da kan iyalai, da kuma tabbatar da cewa duk wani yaro da ya cancanta ya samu maganin zazzaɓin cizon sauro.

    Gwamna Aliyu ya ce a wani bangare na kokarin tallafa wa dukkan harkokin kiwon lafiyar al’umma, gwamnati ta samar da babura ga ɗaukacin jami’an shirin ‘Roll Back Malaria’ da ke faɗin ƙananan hukumomin jihar guda 23.

    A nasa jawabin wakilin Sarkin musulmi kuma hakimin Wurno, Alhaji Alhassan Cigari, ya ce shirin zai taimaka sosai wajen hana yara kamuwa da cutar zazzaɓin cizon sauro.

    Ya kuma jaddada aniyar sarakunan gargajiya a jihar na tallafawa duk wani shiri da ke da nufin kare lafiyar al’umma.

  6. Ƴan Burtaniya da Taliban ke tsare da su na iya mutuwa a kurkuku, in ji ɗansu

    ...

    Asalin hoton, PA Media

    Yaron wasu ma'aurata ƴan Burtaniya da ƴan Taliban suka tsare watanni biyar da suka gabata ya shaida wa BBC cewa yana fargabar za su mutu a gidan yari.

    An kama Peter Reynolds mai shekara 80 da Barbie mai shekara 76 a ranar 1 ga watan Fabrairu yayin da suke komawa gidansu da ke tsakiyar lardin Bamiyan na ƙasar Afganistan.

    Ba a dai san takamaiman dalilin da ya sa aka tsare su ba.

    Ɗan su Jonathan Reynolds ya ce lafiyarsu na ƙara taɓarɓarewa cikin sauri, sakamakon ƙarancin abinci da ƙarancin abinci mai gina jiki.

    Ministan harkokin waje na Taliban ya ce suna samun kulawar likitoci kuma "ana nan ana ƙoƙarin ganin an sako su, amma ba a kammala ba".

    Mista Reynolds ya ce ya kasance a cikin wani mawuyacin hali, yayin da ya shafe watanni biyar yana jiran a sako iyayensa, waɗanda suka zauna a Afghanistan na tsawon shekara 18, inda suke da takardar zama ƴan ƙasa suna kuma gudanar da ayyukan bunƙasa ilimi.

    Mista Reynolds ya ce an tsare iyayensa cikin mawuyacin hali - duk da cewa alƙali ya ce "ba su da wani laifi" kuma ba sa fuskantar wata tuhuma.

  7. Ƴancin cin gashin kai wajen yaƙi da cin hanci na tayar da ƙura a Ukraine

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Ukraine na fuskantar suka bayan da shugaban ƙasar Volodymyr Zelensky ya rattaba hannu kan wata doka da ta taƙaita ƴancin cin gashin kan hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa guda biyu.

    Ƙudirin dokar mai cike da cece-kuce ya mayar da hukumomin biyu, Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (NABU) da kuma ofishin masu gabatar da ƙara na musamman (SAP) ƙarƙashin ofishin babban mai gabatar da ƙara, wanda shugaban ƙasa ke naɗawa.

    Zelensky ya bayar da hujjar cewa akwai buƙatar ɗaukar matakan gaggawa saboda NABU da SAP suna barin shari'ar laifuka su kwashe tsawon shekaru a kotu, ya kuma dage kan cewa dole ne a kuɓutar da su daga ƙarkashin tasirin Rasha.

    Ya sanya hannu kan ƙudirin dokar a ranar Talata bayan ya samu goyon bayan ƴan majalisa 263 daga cikin 324.

    A daren Talata dubban mutane ne suka taru a wajen ofishin shugaban ƙasar da ke Kyiv don yin zanga-zangar adawa da dokar.

    An kuma gudanar da ƙananan gangami a biranen Odesa da Dnipro da Lviv da Sumy - duk da cewa ana ci gaba da fuskantar barazanar hare-haren jiragen saman Rasha. T

    Taron dai shi ne zanga-zangar adawa da gwamnati ta farko tun bayan da Moscow ta ƙaddamar da cikakken mamayar Ukraine a shekarar 2022.

  8. Afirka za ta fuskanci ƙarin matsaloli bayan rage tallafin da Burtaniya ke bayarwa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Biritaniya ta bayyana shirinta na rage tallafin da ta ke bai wa ƙasashen ƙetare, yayin da za ta zaftare tallafin da ta ke bai wa ɓangaren ilmin yara da kuma lafiyar mata a Afirka da ke fuskantar raguwa mafi girma.

    Tun a watan Fabrairu gwamnatin ta sanar cewa za ta zaftare kuɗaɗen tallafin da ta ke bayarwa a ƙasashen waje da kashi 40 cikin 100 - a cikin shekara uku masu zuwa domin ta samu damar kashe ƙarin kuɗi a ɓangaren tsaronta.

    Rahoton Ofishin harkokin wajen Burtaniya ya ce lamarin zai fi shafar ƙasashen Afrika, inda za a rage yawan kudin da ake kashewa a fannin lafiyar mata da kuma tsaftace ruwan sha, abin da ake gani zai iya janyo karuwar cututtuka da mace-mace.

    Sa'annan za a zaftare kuɗi mai yawan gaske a fannin ilimin ƙananan yara.

    Burtaniyar kuma za ta rage kudin da ta ken tallafawa yankunan Falasɗinawa da aka mamaye, inda za a zaftare kashi 21 cikin 100 duk da cewa a baya ta yi alƙawarin da za ta rage ba.

    Ministar kula da ayyukan ci gaba Lady Chapman, ta ce ba za a taɓa kuɗaɗen da ake bai wa ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa ba irinisu GAVI Vaccine da kuma bankin duniya.

    Haɗakar ƙungiyoyin jin-ƙai a Biurtaniya ta ce mata da kanana yara daga ƙasashen da ke fama da talauci ne, wannan matakin zai fi yi wa illa.

  9. Jami’in Habasha ya musanta iƙirarin Trump kan gina madatsar ruwan kogin Nilu

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani jami’in ƙasar Habasha ya musanta iƙirarin Donald Trump na cewa Amurka ta taimaka wajen samar da kuɗin gina sabuwar gagarumar madatsar da ƙasar Habasha ta yi a kogin Nilu, yana mai cewa ƙarya ne kuma labari ne da zai haifar da ɓarna.

    A makon da ya gabata, Shugaba Trump ya ce an gina madatsar ruwan da ake cece-kuce da “kudin Amurka”.

    Aikin wanda aka fi sani da Grand Ethiopian Renaissance Dam (Gerd), shi ne babban kamfanin samar da wutar lantarki a Afirka kuma babban abin alfahari ga Habashawa.

    A cikin shekara 14 da aka kwashe ana kammala Gerd, hukumomin Habasha sun sha nanata cewa gwamnati ce ta ɗauki nauyin gina madatsar ruwan, tare da gudunmawar al'ummar Habasha.

    Sai dai madatsar ruwan ta fusata ƙasashen Masar da Sudan da ke gabar kogin Nilu kuma suna fargabar cewa madatsar ruwan na iya haifar da ƙarancin ruwa a cikin ƙasashensu.

    BBC ta buƙaci fadar White House ta ta yi karin bayani kan kalaman Trump.

    A ranar Talata, Fikrte Tamir, mataimakin darektan ofishin kula da harkokin Gerd, ya yi watsi da kalaman na Trump, yana mai cewa an gina madatsar ruwan “ba tare da wani taimako daga ƙasashen waje ba”.

    Wannan dai ba shi ne karon farko da Trump ke iƙirarin hannun Amurka a Gerd ba.

    A watan da ya gabata, a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na dandalin sada zumunta na Truth Social, shugaban ya ce "Amurka ce ta ɗauki nauyin gina madatsar ruwa" kuma "yana rage yawan ruwan da ke kwarara daga cikin kogin Nilu".

  10. WFP zai dakatar da tallafin abinci a Arewa maso Gabashin Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa daga ƙarshen watan Yuli, zai dakatar da tallafin gaggawa na abinci da kiwon lafiya ga mutum miliyan 1.3 a arewa maso gabashin Najeriya saboda ƙarancin kuɗi.

    Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da tashe-tashen hankula ke ƙaruwa, kuma yunwa na kai matsayi mafi muni a tarihin ƙasar.

    WFP ya ce kayan abinci da na kiwon lafiya sun ƙare gaba ɗaya, kuma rabon da ake yi yanzu shi ne na ƙarshe.

    Idan ba a samu tallafi cikin gaggawa ba, mutane da dama za su fuskanci yunwa, gudun hijira ko kuma shiga hannun ‘yan tada ƙayar baya.

    Daraktan WFP a Najeriya, David Stevenson, ya ce kusan mutum miliyan 31 ke fama da matsanancin yunwa a ƙasar wanda shine mafi yawa a tarihi.

    "Yara ƙanana za su fi shan wahala, domin fiye da asibitoci 150 a Borno da Yobe da ke kula da yara ƙasa da shekaru biyu za su rufe." in ji daraktan.

    WFP na buƙatar dala miliyan 130 domin cigaba da ayyukanta har zuwa ƙarshen shekarar 2025.

  11. Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Bindiga fiye da 100 a jihar Neja

    ..

    Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta tare da haɗin gwiwar ƴan sa-kai waɗanda ake kira bijilanti sun samu nasara a wata fafatawa da suka yi da ƴan bindiga a ƙauyen Warari da ke Jihar Neja.

    Rundunar ta ce a lokacin artabun, wadda ta faru a jiya Talata ta kashe fiye da ‘yan bindiga 100 waɗanda ke gilmawa a kan babura.

    Lamarin ya faru ne bayan da sojojin suka samu sahihan bayanai daga mazauna yankin game da hanyoyin da ‘yan bindiga ke bi don satar shanu.

    Wannan ne ya bai wa sojojin damar kitsa kwanton-ɓauna da ya kai ga fafatawar da ta kai ga hallaka ƴan bindigan da dama.

    Jaridar PRNigeria ta ambato shaidun da suka ce sojojin sun yi amfani da motoci masu sulke da makamai na zamani wanda ya ba su galaba a kan ‘yan bindigar.

    Shugabannin al’umma a Warari sun tabbatar da girman rashin da ‘yan bindigar suka tafka, inda suka bayyana cewa gawarwakin wasu daga cikin su sun bazu a tituna da gonaki da dazuka da ke kewaye da yankin.

    Neja na cikin jihohin Najeriya da ke fama da hare-haren ƴan bindiga masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

  12. Peter Obi na da masaniya kan ziyarar da na kai wa Abure - Datti

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Datti Baba-Ahmed, ya ce jagoran jam'iyyar, Peter Obi, na da masaniya kan matakin da ya ɗauka na halartar taron ɓarin jam'iyyar da ke ƙarƙashin shugabancin Julius Abure.

    Datti ya ce ya ɗauki matakin ne a wani yunƙuri na sulhunta ƴaƴan jam’iyyar da suka fusata.

    Datti ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels, bayan ziyarar tasa ta janyo ce-ce-ku-ce.

    “Jam’iyyar Labour ba jam’iyya ba ce da za a yi watsi da ita, ko a gudu daga cikinta, ko a yi watsi da muhimmancinta ba," in ji Datti.

    “Ina tabbatar muku cewa kowanne mataki da nake ɗauka, ɗaukacin masu ruwa da tsaki (na jam'iyyar) na da masaniya a kai. Ba sai na shiga yin bayani dalla-dalla kan yadda muke gudanar da harkokinmu ba."

    Datti ya ce ya je taron ne don haɗa kan ƴaƴan jam'iyyar da kuma neman kawo sulhu.

    Jam'iyyar LP ta shafe tsawon lokaci tana fama da rikicin cikin gida, lamarin da ya sanya aka samu ɓari biyu a jam'iyyar, inda kowanne ke ikirarin kasancewa halastacce.

    Ɓarin da ke ƙarƙashin jagorancin Abure, a baya-bayan nan ya bai wa Obi wa'adin ficewa daga jam'iyyar sanadiyyar rawar da yake takawa a hadakar da ƴan hamayya ke ƙoƙarin samarwa.

    Peter Obi ya fi karkata ɓagaren shugabancin Nenadi Usman, wadda aka zaɓa bayan iƙirarin cewa wa'adin shugabancin Julius Abure ya ƙare.

  13. Za a yi tattakin neman sakin Mohamed Bazoum a Nijar

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Wata ƙungiyar fararen hula ta MINNJE a Jamhuriyar Nijar na shirin gudanar da tattaki a babban birnin ƙasar, Niamey, a ranar 27 ga Yuli domin neman a saki tsohon shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum, wanda ke tsare tun ranar 26 ga Yuli, 2023.

    Ƙungiyar ta sanar da hukumomi a ranar 21 ga Yuli cewa za ta gudanar da tattaki ta lumana domin neman a saki Bazoum ba tare da wani sharaɗi ba.

    Jagoran ƙungiyar, AbdoulRahaman Ide a tattaunawarsa da BBC ya bayyana dalilansu na yin wannan kira.

    "Abin da yasa muke so a saki Bozoum shine mun ga kamar riƙe shin da ake yi ba bisa ƙa'ida bane, bai kamata a riƙe shi ba haka na dindindin ba tare da shari'a ba." in ji jagoran.

    "Saboda hake muna kira ga gwamnatin sojin ƙsar da su sake shi ko kuma suyi masa shari'a."

    "Muna kuma hanƙoran ganin ɓangaren shari'aya ya tsaya da ƙafarsa, da gurfanar da waɗanda ake zargi da yin zagwon ƙasa da tattalin arziƙin ƙasa, da kuma ƙarfafa dakarun tsaron ƙasar wajen yaƙi da ta'addanci" jagoran ya ƙara da cewa.

    An dai tsare Bazoum da matarsa ne a gidansu tun bayan juyin mulkin da hamɓarar da shi daga mulki, wanda ya bai wa Janar Abdourahamane Tchiani mai shekaru 65 damar karɓar mulki.

  14. Mutum 10 sun mutu cikin sa’o’i 24 saboda yunwa — Ma’aikatar lafiya Hamas

    Ma’aikatar Lafiyar Hamas ta bayyana cewa ƙarin mutum 10 ne suka mutu cikin sa’o’i 24 da suka gabata sakamakon yunwa a Gaza.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar, ma’aikatar ta ce hakan ya kai adadin mutanen da suka mutu saboda yunwa zuwa 111 tun bayan harin 7 ga Oktoba, 2023.

  15. Ana shirin haramta wa ma'aikatan gwamnati kai ƴaƴansu makarantun kuɗi a Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/Facebook

    Majalisar Wakilai ta gabatar da wani ƙudirin da ke neman haramta wa ma’aikatan gwamnati da iyalansu zuwa makarantu da asibitoci masu zaman kansu.

    Wanda ya gabatar da Amobi Ogah, ya ce ƙudirin zai tilasta wa jami’an gwamnati amfani da makarantu da asibitocin gwamnati domin farfado da inganci da amincewa da su.

    Ya ce barin jami’an gwamnati zuwa cibiyoyin masu zaman kansu da na ƙasashen waje na daga cikin dalilan durƙushewar makarantun da asibitocin gwamnati.

    Ogah ya bayyana cewa "Ƴan Najeriya sun kashe kuɗi fiye da dala biliyan 29 wajen neman magani a asibitocin ƙasashen waje a zamanin Shugaba Buhari, da kuma fiye da dala miliyan 218 wajen karatu a waje a shekarar 2023 kacal."

    Ya ce ƙudirin zai taimaka wajen rage fita ƙasashen waje neman magani ko ilimi, da kuma dawo da martabar cibiyoyin gwamnati.

  16. An sallami gwamna Dikko Radda daga asibiti

    ...

    Asalin hoton, Dr. Dikko Umaru Radda/Facebook

    An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, daga asibiti bayan an tabbatar da ya samu sauƙi daga raunin da ya samu sakamakon hatsarin mota a hanyarsa daga Katsina zuwa Daura.

    Gwamnan ya samu kulawa ta musamman daga masana lafiya, kuma yanzu an tabbatar da cewa ya dace da komawa bakin aiki ba tare da wata matsala ba.

    A cewar wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar, likitan da ke kula da lafiyar gwamnan ya tabbatar da cewa ya samu sauƙi sosai, kuma ya shirya tsaf don ci gaba da gudanar da ayyukan mulkinsa.

    Bayanin da gwamnatin jihar dai ta fitar game da hatsarin ta ce lamarin ya faru ne a lokacin da gwamna Radda ke kan hanyarsa ta zuwa Daura, inda wata mota ƙirar Golf ta kauce hanyarta, kuma ta faɗa wa motar da gwamnan ke ciki.

  17. Aƙalla Falasɗinawa 17 sun mutu a hare-haren sama da Isra’ila ta kai a Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutum 17 ciki har da yara huɗu da jariri ɗaya ne suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren sama da Isra’ila ta kai a Zirin Gaza tun daga safiyar Laraba, in ji mai magana da yawun Ma’aikatar Ceton Gaggawa da Hamas ke jagoranta a Gaza.

    Mai magana da yawun ya ce hare-haren sun shafi wurare uku daban-daban, inda aka kai hari kan gidaje biyu da wani sansanin tanti, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 17, ciki har da mutum takwas daga iyali ɗaya.

    Haka kuma, mutum 24 sun jikkata a hare-haren, a cewar kakakin.

    Ƙungiyoyin ceto na ci gaba da aikin tono gawawwaki da taimaka wa waɗanda suka jikkata a wuraren da hare-haren suka afku.

    Sojojin Isra’ila ba su ce komai ba tukuna game da wannan lamari.

  18. Majalisar dattawa ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

    ...

    Asalin hoton, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/Facebook

    A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ciyo bashin kuɗi daga ƙasashen waje da ya kai sama da dala biliyan 21 domin kashewa tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026

    Amincewar ta biyo bayan gabatar da rahoton kwamitin majalisar dattawa kan bashi daga cikin gida da waje, wanda shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Wamakko, ya gabatar.

    Akwai kuma shirin tara dala biliyan 2 daga cikin gida.

    Tinubu ya ce za ayi amfani da bashin kuɗaɗen ne kan ɓangarorin gine-gine da noma da tsaro da wutar lantarki da fasahar sadarwa.

    An ware dala biliyan 3 don farfaɗo da layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri.

    Sanatoci da dama sun goyi bayan wannan shirin, inda suka ce hakan yana nuna adalci ga kowane yanki na ƙasar, kuma yana cikin tsarin da duniya ke bi wajen ci gaban tattalin arziki.

  19. Amurka za ta rage wa Japan haraji bayan sun cimma yarjejeniyar kasuwanci

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Amurka da Japan sun amince da wata jarjejniyar kasuwanci inda Donald Trump ya amince ya rage barazanar harajinsa na kashi 25 ga kayayakkin Japan.

    Yarjejeniyar ta samar da sassauci ga masana'antar ƙera motoci mai mahimmanci ga Japan, tare da rage harajin zuwa kashi goma sha biyar cikin ɗari.

    Sanarwar ta sa hannayen jarin Japan da Koriya ta Kudu sun ƙaru musamman na kamfanonin kera motoci - Toyota da Nissan da Honda.

    Trump ya ce Japan ta amince ta zuba jari a Amurka da kuma buɗe ƙofa ga kayyyakin Amurka

  20. Ƙungiyoyin agaji fiye da 100 sun gargaɗi cewa yunwa na ƙara ƙamari a Gaza

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Ƙungiyoyin agaji sama da ɗari sun fitar da wata sanarwar hadin gwiwa inda suka yi gargaɗin cewa yunwa na ƙara ƙamari a Zirin Gaza, duk kuwa da ƙaryatarwar da Isra'ila ke yi.

    Wadanda suka sa hannu kan sanarwar sun ƙunshi har da ƙungiyar likitoci ta Doctors Without Borders, da Save the Children da kuma Oxfam.

    Sun yi kira da a ɗauki matakin gaggauawa domin ceto rayukan Falasɗinawa kafin a kai ga rasa sauran waɗanda za a ceto.

    Jami'an Isra'ila sun amince cewa an samu raguwar kayayyakin da suke shigarwa Gaza. Amma sun yi watsi da abin da suka kira rahotannin farfaganda na yawan mutanen da suka mutu sakamakon rashin abinci