Father Mbaka: An lakaɗa wa ma'aikatan BBC duka a wata cocin Enugu

FATHER MBAKA

Asalin hoton, AMEN.

Wani malamin Cocin Katolika da ke Najeriya, Rev Fr. Ejike Mbaka tare da wasu mambobin cocinsa sun ci zarafin wasu ma'aikatan BBC biyu tare da direbansu ranar Laraba da yamma, a jihar Enugu, da ke Kudu maso Gabashin kasar.

'Yan jaridar, Chioma Obianinwa, da Nnamdi Agbanelo da direbansu, Ndubuisi Nwafor, sun samu rakiyar wani malami Rev Cajethan Obiekezie da ya shige musu gaba domin yin hira da Mbaka.

Lokacin da tawagar BBC ta isa cocin Adoration Ministry wadda Father Mbaka ke gabatar da wa'azi da misalin karfe 10 na safe, ba ta samu yin hira da shi ba.

Sai dai tawagar tamu ta sake bin sa gida da misalin karfe 5 na yamma domin tattaunawa da shi, bisa rakiyar Rabaran Obiekezie.

A lokacin ne wasu muƙarraban Mbaka kusan mutum 20 suka kewaye wakilanmu da ke ƙofar gidan suna jira a mota bayan da Obiekezie ya shiga gidan domin sanar da shi.

A cewar Obianinwa, "Mutanen sun kwace kayan aikinsu kuma sun yi barazanar kashe su saboda rubuta 'munanan labarai game da Mbaka.'

Mutanen da ke wajen gidansa sun ce BBC News Igbo na rubuta munanan labarai a kan Mbaka kuma suka fara dukan Nnamdi, da Solomon da Ndubuisi.

Wakiliyar BBC ta ci gaba da cewa Mbaka da Obiekezie sun fito daga gida lokacin da suka ji hayaniya, sai Mbaka ya fuskance ta ya fara nuna ta da yatsa yana kiranta da 'shaidaniya.'

"Wannan ne yasa mukarraban nasa suka tunzura, suka ci gaba da dukanmu. Ya nemi mutanensa su kwace wayoyinmu da kyamarorinmu. Sun ce za su kashe mu, kuma ba abinda aka iya a yi a kan hakan. Ravan Obieikezie na cewa su daina, sai suka rufe shi da suka shima, suka kwace wayarsa" in ji ta.

Obianinwa ta ce mutanen su tsaya da dukansu a lokacin da ta yi kururuwa cewa "duniya za ta san cewa an kashe su a gidan Mbaka."

"A wannan lokacin, Rev Mbaka ya nemi mu bar wurin kafin mutanensa su kashe mu. Ya bukace su da su dawo mana da kayan aikinmu sannan suka fatattake mu daga harabar. Mutanensa sun bi mu har sai da muka bar jihar," in ji ta.

Lokacin da BBC ta kira lambar Mbaka da aka sanya a shafinsa na sada zumunta na Facebook, mun tarar layin a kashe.