Me ya sa Amurka ke son tattaunawa da Taliban?

Bayan an shafe watanni ana tattaunawa tsakanin 'yan Taliban da Amurka, da alama kwalliya za ta biya kudin sabulu.
A wannan karon, ana ganin tattaunawar ta kai wani mataki da muhimmancinta zai iya kawo karshen yaki mafi muni da ya daidaita kasar.
Jakadan Amurka Zalmay Khalilzad a wallafa wani sakon Twitter, "idan 'yan Taliban suka yi abin da ya dace, mu ma zamu yi namu kokarin domin cimma yarjejeniya."
Wakilan kungiyar Taliban sun sanar da BBC cewa suna da karfin gwuiwa, amma da sauran aiki a gaba.
Sannan Taliban ta san Shugaba Trump na son mai da sojojin Amurka gida kafin zaben shugaban kasa da za a yi a badi.
Amma duk da sanin haka, Mista Khalilzad ya cigaba da nanata cewa Amurka za ta janye ne kawai bayan an biya ma ta wasu bukatu - wato tabbaci cewa ba za a sake tsunduma kasar cikin wani yakin da ya fi wannan muni ba.







