Tinubu ya yaba wa sojojin Najeriya da na Amurka kan kisan Al-Manuki

Asalin hoton, Bola Tinubu/X
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yaba wa abin da ya kira nasarar hare-haren haɗin gwiwa tsakanin dakarun ƙasarsa da na Amurka wajen kisan mataimakin shugaban ISIS na duniya.
Cikin wata sanarwa da Shugaba Tinubu ya fitar ranar Asabar ya ce harin da sojojin suka kai ranar Juma'a kan mayaƙan IS ya haifar da kisan Abu-Bilal Al-Manuki tare da wasu mayaƙansa.
A cewar Tinubu, harin ya faɗa kan gidan Abu-Bilal Al-Manuki da ke yankin tafkin Chadi.
“Ƙoƙarin sojojin Najeriya sun yi aiki tare da dakarun Amurka, wajen shirya harin haɗin gwiwa da ya haifar da mummunan ɓarna kan manyan jiga-jigan ƙungiyar ISIS.''
Shugaba Tinubu ya gode wa Amurka kan goyon bayan da suke bayarwa a lamarin.


