Borno ta ga bala'o'i kala-kala - Zulum

Borno ta ga bala'o'i kala-kala - Zulum

Gwamnan jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya Babagana Umara Zulum ya ce al'ummar jihar na ci gaba da gode wa Allah duk da irin bala'o'in da jihar ta fuskanta.

"Abin akwai wahala, sai dai Allah ba ya ɗora wa mutum abin da ba zai iya ba.

"Ga rashin kuɗi ga masifa da muka gani kala-kala, ga ambaliyar da aka yi fama da ita."

Gwamnan ya fadi hakan ne a tattaunawar da ya yi da BBC shekara ɗaya bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta faru a birnin Maiduguri.

Ambaliyar ta tilasta wa dubban mutane barin muhallansu a babban birnin jihar, Maiduguri sakamakon fashewar madatsar ruwa ta Alau, kuma lamarin ya haifdar da asarar rayuka da dama.

Shekara ɗaya bayan haka, Babagana Zulum ya shaida wa BBC cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakan ganin cewa irin haka ba ta faru ba a wannan shekara.

Borno na cikin jihohin da hukumar lutra da yanayi ta Najeriya, Nimet ta yi gargadin cewa za a iya fuskantar ambaliyar ruwa a daminar 2025.

A yanzu gwamnatin jihar Borno ta gudanar da aikin faɗaɗawa da yashe madatsar ruwa ta Alau, inda daga can ne ruwan ya yi ambaliya a 2024.

Borno ce cibiyar rikicin Boko Haram, wanda aka kwashe kimanin shekara 15 ana fama da shi.

Rikicin ya haddasa asarar dubban rayuka tare da tarwatsa miliyoyi daga muhallansu.