..Daga Bakin Mai Ita Tare Da Baban Ramota

..Daga Bakin Mai Ita Tare Da Baban Ramota

A wannan makon, BBC ta yi babban kamu inda ta tattauna da fitaccen mai barkwancin nan a fina-finan Kannywood da ake kira Baban Ramota.

Sunansa Alhaji Aƙilu Muhammad amma an fi sanin sa da Baman Mulka ko Baban Ramota.

An haifi Baban Mulka a ranar 25 ga watan Maris na shekarar 1960 a garin Ɗanganjiba da ke ƙaramar hukumar Ƙafur ta jihar Katsina.

Baban Ramota wanda ɗan asalin garin Zazzau ne ya yi firamare da sakandare da kuma NCE duka a jihar Kaduna.

Ya fara harkokin wasan kwaikwayo sakamakon irin yadda fitaccen ɗan wasan kwaikwayon nan na arewacin Najeriya, Usman Baba Patigi ke gudanar da wasanni a Kaduna a shekarun da suka gabata.

Ɗan wasan kwaikwayon ya ce Allah ya hore masa hazaƙar yin salon maganar ƙabilu da dama a wasannin da yake yi.

Sai dai kuma ya ce ba ya jin harshen Yarabanci domin haɗe-haɗe kawai yake yi ya kwaɓa.