Boko Haram: Abin da BBC Hausa ta gano da ta je Zabarmari

Latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

BBC Hausa ta bi tawagar majalisar dinkin duniya zuwa kauyen Zabarmari da ke jihar Boron Najeriya inda mayakan Boko Haram suka kashe gomman mutane a karshen makon jiya.

Jami'an majalisar dinkin duniyar sun ce an kai ziyarar ne da nufi n gano hakikanin abin da ya faru sakamakon kisan manoma fiye da 40 a kauyen.

Mazauna kauyen na Zabarmari sun ce ba su taba fuskantar bala'i irin wannan ba a rayuwarsu.

Sun yi kira ga gwamnatin kasar ta tsaurara matakan tsaro a yankin arewa maso gabashin kasar.

Wannan kisa ya tayar da hankalin 'yan kasar da ma duniya, lamarin da ya kai ga kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya sauka daga mulki.

Wasu bidiyon da za ku so ku kalla