Najeriya ta amince da ɓullo da sabbin matakai don sauƙaƙa rayuwa

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. 'Mutanen Ghana fiye da dubu 800 sun auka cikin talauci a 2022'

    Bankin Duniya ya ce 'yan Ghana kimanin 850,000 ne aka jefa su cikin talauci bara, saboda tsadar rayuwa sanadin rashin kuɗin sayen kaya da ƙarin farashin abinci da kayan masarufi.

    A cikin sabon rahoton Nkechi Ogbonna, wakiliyar kasuwancin Afirka ta Yamma, a kan Tattalin Arzikin Ghana mai suna: Tattalin Arziki: warware hauhawar farashin kaya a Kan Talauci da Wadatar Abinci, Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Ghana ya shiga mawuyacin hali saboda faduwar darajar cedi da hauhawar farashi da kuma karyewar jarin da ake juyawa a cikin gida a 2022.

    Lamarin ya faru ne bayan ya fara farfaɗowa daga annobar korona a 2021.

    Bankin ya ce hukumomi sun gaza aiwatar da muhimman sauye-sauye masu ɗorewa da ake bukata da nufin dawo da basuka da dorewar tattalin arziki a 2022 wanda ya samu ci gaba gaba ɗaya da kashi 3.1%, lamarin da ke nuna cewa ya ragu matuka daga kashi 5.4% da aka samu a shekarar da ta gabata.

    Masana tattalin arziki a bankin sun ce hauhawar farashi, ya haifar da matsin rayuwa, da kuma ƙaranci wanda ya kai mafi girma cikin shekara 20 da kashi 54.1 a watan Disamban 2022.

    Wani ɓangare na rahoton ya ce, yayin da farashin kayan abinci ke hauhawa, 'yan Ghana da dama sun ƙoƙarta wajen sayen abincin da ya dace da buƙatunsu abin da hakan ya nuna tsananin ƙarancin abincin da aka shiga.

    Zuwa watannin uku na ƙarshen 2022, ana jin cewa kashi ɗaya cikin huɗu na jama'ar Ghana ba su da isasshen abinci, kuma ana sa ran adadinsu zai ci gaba da ƙaruwa a 2023.

    A matsayinta na ƙasa mafi arziƙin zinari a Afirka, Ghana ta samu dala miliyan 600 cikin dala biliyan 3 daga asusun ba da lamuni na duniya da nufin daidaita tattalin arzikinta yayin da ta fara sake fasalin basuka da sauran manufofin tattalin arziki da nufin bunkasa kudaden shiga.

  2. Mu kasance lafiya

    To a nan za mu dakatar da kawo muku labarai da rahotanni a wannan shafi na kai tsaye daga sassan duniya. Da fatan kun ji daɗin kasancewa da mu. Sai gobe idan Allah ya kai mu za mu dawo.

    Amma dai kuna iya gangarawa cikin wannan shafi, don ci gaba da karanta rahotannin da muka wallafa muku.

    Mukhtari Adamu Bawa ke cewa asuba tagari!

  3. Indiya ta dakatar da fitar da shinkafa zuwa ƙasashen waje

    rice farm

    Asalin hoton, Getty Images

    Indiya ta hana fitar da farar shinkafa wadda ba basmati ba, zuwa ƙasashen waje a wani yunƙuri na daƙile hauhawar farashin da za a iya fuskanta a cikin gida.

    Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya ya lalata amfanin gona a ƙasar kuma farashin shinkafa tuni ya tashi zuwa sama da kashi 11% a tsawon wata 12 da ta wuce.

    Shinkafa fara wadda ba basmati ba a yanzu ta kai yawan kashi ɗaya cikin huɗu na shinkafar da Indiya take fitarwa zuwa ƙasashen waje, a cewar ma'aikatar harkokin masu sayen kaya wadda ta ba da sanarwar samun canji.

    Ƙwararru sun yi gargaɗin cewa matakin na iya janyo tashin farashin abinci a duniya.

    "Ba ganganci ba ne idan aka ce wannan mataki zai iya yin tasiri kan farashin abinci a duniya," cewar Emma Wall, shugabar sharhi kan harkokin zuba jari da bincike a Cibiyar Hargreaves Lansdown.

    Harkar safarar abinci tuni yake fuskantar matsin lamba, bayan Rasha ta janye daga wata yarjejeniya a wannan mako da ke tabbatar da samun hanya amintacciya ga hatsin da ke fitowa daga Ukraine, ciki har da alkama.

    Indiya ita ce ƙasar da ta fi fitar da shinkafa zuwa ƙetare, inda take safarar fiye da kashi 40% na shinkafa ga duniya. Shinkafar da ba basmati ba akasari ana kai ta ƙasashen Asiya da Afirka ne.

  4. Najeriya ta amince da ɓullo da sabbin matakai don sauƙaƙa rayuwa

    VP Nigeria

    Asalin hoton, Kashim Shettima/Facebook

    Majalisar kula da Tattalin Arziƙi a Najeriya ta sanar da wasu sabbin matakai da gwamnati za ta ɗauka don samar wa ‘yan ƙasar sauƙin rayuwa sanadin wahalhalun janye tallafin man fetur.

    Majalisar ta sanar da matakan ne a ƙarshen taron wata-wata da ta yi a ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima.

    Taron na tsawon kimanin sa’a shida ya fi mayar da hankali a kan batutuwa guda biyu da suka fi tasiri wajen jefa ‘yan ƙasar cikin mawuyacin hali. Wato janye tallafin mai da kuma karyewar darajar naira.

    Bayan tafka muhawara da musayar yawu, taron ya amince da ɗaukar wasu matakai na gaggawa domin tsamo ‘yan Najeriya musamman mafi ya rauni daga cikin halin da suka shiga. Daga ciki akwai buƙatar kowacce jihar ta tsara yadda za ta samar wa jama’arta sauƙi ko dai ta hanyar raba tallafin kuɗi ko kuma ta hanyar da ta fi dacewa.

    Haka ma an amince da bai wa ma'aikatan gwamnati tallafin kuɗi a kan albashinsu, tsawo wata shida, sannan kowacce jiha ta tabbatar ta biya ma'aikata da ‘yan fansho dukkan basukan da suke bi.

    Waɗannan in ji majalisar za a aiwatar da su ne ta hanyar amfani da rarar kuɗin da gwamnati za ta samu saboda janye tallafin man fetur da kuma daidaita harkar canjin kuɗi.

    Bugu da ƙari, taron ya amince da aiwatar da wani tsari na sauya makamashin da ababen hawa suka fi amfani da su daga man fetur wanda ya yi tsada yanzu zuwa wani nau'in iskar gas da ake kira CNG a taƙaice wanda Najeriya ke da shi mai tarin yawa kuma ga arha.

    Jihohin ƙasar sun amince za su fara juya motocin jigilar ma’aikata zuwa masu amfani da iskar gas.

    Amma duk waɗannan matakai, sai bayan an aiwatar da shirin raba kayan abinci ga ɗaukacin jihohin ƙasar domin sauko da farashinsa, a cewar Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.

    Majalisar dai ta ce tana sane da mawuyacin halin da ‘yan ƙasar ke ciki don haka ɗaukar waɗannan matakai sun zama wajibi domin kaucewa yanayin da wahala za ta tura ‘yan ƙasar bango har su yi bore.

    Wani babban batu da ‘yan kasar ga alama suke son su ji matsayar majalisar a kai shi ne amincewa ko akasin haka da bukatar ƙarin albashi ga ma’aikata zuwa aƙalla N200,000 kamar yadda ‘yan kwadago ke nema, sai dai ga alama babu wata matsaya da aka cimma a kan haka.

  5. Hizba ta fara raba fom don auren zawarawa a Kano

    Daurawa

    Asalin hoton, Sheikh Daurawa/Facebook

    Hukumar Hisba a jihar Kano ta ce ta kafa kwamitoci guda biyu waɗanda za su yi aikin rabon fom da tantance lafiyar masu buƙatar shiga shirinta na auren zawarawa da 'yan mata.

    Ta ce shirye-shiryen sun yi nisa, tun bayan samun amincewar gwamnatin Kano na gudanar da shirin auren zawarawa da ‘yan mata 1,800.

    Shugaban Hizba ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce za a bai wa ƙananan hukumomin cikin birnin Kano takwas, gurbin mutum hamsin kowacce, yayin da ƙananan hukumomin wajen birni kuma za a ba su gurbin mutum 30.

    Fitaccen malamin ya ce idan mutum yana da sha'awar shiga shirin, da farko zai je ya karɓi fom. Sannan a cike bayanai muhimmai da hukumar Hizba take buƙata guda shida.

    "Na farko", in ji Sheikh Daurawa, "mu san asalin mutum. Na biyu mu san sana'arsa, mu san halayensa, sannan mu tantance lafiyarsa."

    "Sannan ya kawo mutum da za su ba da shaida a kansa cewa (shi) mutumin kirki ne. Sannan kuma ya zama mun samu cikakken bayani dangane da inda yake zama," cewar shugaban na Hizba.

    Ya ce hukumarsu ba haɗa auren za ta yi ba, ga duk mai sha'awar shiga shirin zai karɓi fo ne bayan ya/ta daidaita da wanda yake/take son aure.

    • Auren zawarawa: An gano maza da mata 18 dauke da HIV
    • Me ya sa ake tsangwamar zawarawa a cikin al'umma?
  6. Farashin alkama ya sake tashi a kasuwar duniya

    Wheat

    Asalin hoton, Getty Images

    Farashin alkama ya yi tashin gwauron zabi a kasuwannin duniya bayan Rasha ta ce za ta ɗauki duk wani jirgi da ya nufi tashar ruwan Ukraine a matsayin wani abin da sojojin za su iya kai wa hari.

    Hukumomin Rasha sun janye daga wata yarjejeniyar Majalisar Ɗinkin Duniya a ranar Litinin da ke tabbatar da amintacciyar hanya ta jigilar hatsi zuwa tsallaken Bahar Aswad.

    A cikin dare na uku, Rasha ta ci gaba da luguden wuta kan cibiyoyin ajiyar hatsin Ukraine da ke Odesa da sauran birane.

    Hukumomin Moscow sun kuma yi gargaɗin cewa daga ranar Alhamis duk jirgin ruwan da ya tafi can za a yi masa kallon wanda ke tare da "gwamnatin Kyiv".

    Wani mai magana da yawun fadar White House Adam Hodge ya nunar cewa Rasha na yunƙurin kai wa jiragen fararen hula hari, sannan ta ɗora alhakin abin a kan Ukraine.

    Rasha ta dasa ƙarin nakiyoyin teku a zagayen tashoshin ruwan Ukraine, in ji shi, a wani ɓangare na shiryayyen ƙoƙari don hujjanta kai wa jiragen fararen hula hari.

    Ship

    Asalin hoton, Reuters

    Fadar Kremlin ta Rasha, ba ta mayar da martani cikin gaggawa kan wannan zargi ba.

    A lokaci guda, yayin wani gargaɗi makamancin wannan ga Rasha, Ukraine ta ce jiragen ruwan da suka nufi Rasha ko tashoshin ruwan da ke ƙarƙashin mamaya a yankin Bahar Aswad, ana iya yi musu kallon jiragen dakon kayan sojoji.

    Farashin alkama a kasuwar musaya ta Turai ya yi tashin gwauron zabi da kashi 8.2% a Larabar nan daga ranar da ta gabata, inda ya kai €253.75 ($284; N224,360) duk tan ɗaya, yayin da farashin masara ya tashi zuwa kashi 5.4%.

  7. Birtaniya za ta mayar wa Najeriya kuɗin da James Ibori ya sace

    James Ibori

    Asalin hoton, Metropolitan Police

    Bayan bin tsare-tsare na sama da shekara 10, a yanzu gwamnatin Birtaniya ta kusan kammala ɗaukar matakan mayar wa Najeriya kuɗin da tsohon gwamnan jihar Delta James Ibori ya sace, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ta ruwaito.

    Reuters ya ambato mai shigar da ƙara na Birtaniya na faɗa wa kotun cewa ƙasar za ta karɓo dala miliyan 129 daga hannun Mista Ibori.

    A baya, masu shigar da ƙara sun ce James Ibori ya sace kimamin dala miliyan 165 daga jihar Delta mai arziƙin man fetur ta kudu maso kudancin Najeriya.

    Shekara biyu da ta wuce ne, Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 da tsohon gwamnan ya sace.

    A 2012 ne, aka tusa keyarsa daga Dubai zuwa Birtaniya, inda aka tuhume shi kan laifuka 10 da ke da alaƙa da zambar kuɗi. Bayan ya yi zaman gidan yari na wasu shekaru a Birtaniya, Ibori ya koma Najeriya a 2017.

    A cikin wani gajeren saƙo da ya aike wa Reuters, Mista Ibori ya ce zai ɗaukaka ƙara kan umarnin ƙwace kuɗaɗen nasa da kotun ta bayar.

    A ranar Juma'a ake sa ran fara mayar da kudin kamar yadda Reuters ya bayyana.

    Birtaniya ta samu tsohon gwamnan da laifin satar kuɗaɗen tare da yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 13 a gidan yari a shekara ta 2012.

    Tsohon gwamnan, ya amsa laifi a gaban kotun London, bisa jerin tuhume-tuhume goma da aka yi masa na haramta kuɗaɗen haram, da kuma haɗa baki domin tafka zamba.

    Wannan ne karo na biyu da za a mayar wa Najeriya kuɗaɗen da tsohon gwamnan ya sace, bayan Birtaniya ta mayar wa Najeriya dala miliyan 5.8 a 2021 na almundahanar tsohon gwamnan.

    A 2016, gwamnatocin Najeriya da Birtaniya suka sa hannun kan yarjejeniyar mayar da kuɗaden da masu laifi suka sace.

    • Ayyukan da Najeriya za ta yi da kuɗaɗen da Birtaniya ta ƙwato daga James Ibori
  8. Masu ra'ajin kare ɗan'adam na son a dakatar da hukuncin kisa kan gwarzon ɗan damben Iran.

    Kungiyoyin kare hakkin bil Adama akalla 80 sun yi kira ga shugaban hukumar kare hakkin dan Adam ta majalisar dinkin duniya, Volker Turk ya dakatar da aiwatar da hukuncin kisa kan tsohon gwarzon dan wasan Boxing a Iran.

    A ranar Laraba aka tabbatar da hukuncin kisa a kan Mohammed Javad Vafai-Sani, kuma aka tura shi sashen zartar da hukuncin kisan a gidan yari a Mashhad.

    Fiye da shekara uku kenan da aka kama Vafai-Sani saboda shigarsa zanga-zangar kin jinin gwamnati a cikin watan Nuwamban shekarar 2019.

    An kuma yanke masa hukuncin kisa bayan kotu ta tabbatar da laifin barnata dukiyar kasa da kuma cin amanar ta.

  9. Australia ta yi nasara kan Ireland

  10. Mutum miliyan ɗaya na fuskantar barazanar yunwa a Burkina Faso

    ,,

    Asalin hoton, AFP

    Kungiyar agaji ta 'International Rescue Committee' ta yi gargadin cewa akalla mutum miliyan guda na fuskantar barazanar yunwa cikin watanni masu zuwa a Burkina Faso, sakamakon rashin tsaro da ke addabar wasu sassan ƙasar.

    A halin yanzu mutum miliyan 2.2, wato a akalla mutum guda cikin 10 ne na al'ummar ƙasar ke fuskantar barazanar yunwa a ƙasar.

    To sai dai kungiyar ta IRC ta adadin zai kai miliyan 3.3 cikin watan Satumba mai zuwa.

    A yanzu haka an tsayar da safarar abinci a wasu sassan ƙasar, yayin da aka rufe asibitoci masu yawa, sakamakon tashe-tashen hankula a wasu yankunan ƙasar.

    Kungiyar ta nuna damuw kan halin da ake cikin a garin Djibo da ke arewacin kasar, inda mutum fiye da 200,000 ke neman mafaka a wurin.

    Kasuwannin abinci a yankin sun kasance a rufe, sakamakon rahsin abin sayarwar, yayin da kusan asibitoci hudu daga cikin biyar na yankin suka kasance a rufe.

    A shekarar da ta gabata sojoji 11 ne suka mutu a lokacin da aka yi musu kwantan ɓauna lokacin da suke raka ayarin motocin da ke kai abinci zuwa yankin.

    A halin da ake cikin Burkina Faso na ƙarƙashin jagorancin mulkin soji, inda Kaftin Ibrahim Traoré ke jagorantar gwamnati. A watan Oktoban shekarar da ta gabata ya alƙawarta kwace yankunan ƙasar da ke hannun 'yan bindiga.

  11. Milos Kerkez ya koma Bournemouth

  12. Shettima da gwamnoni na gudanar da taron Majalisar Tattalin Arziki

    Mataimakin shugaban Najeriya

    Asalin hoton, Facebook /Kashim Shettima

    Bayanan hoto, Mataimakin shugaban Najeriya

    Majalisar Tattalin arzikin Najeriya na gudanar da wani taro a fadar gwamnatin kasar da Abuja.

    Taron na samun halartar shugaban majalisar tattalin arzikin, kuma mataimakin shagaban ƙasar Kashim Shettima, da gwamnonin jihohi 36 waɗanda ke zama mambobin kwamitin.

    Rahotonni na cewa taron na samun halartar masu ruwa da tsaki daga bankin Duniya, da sauran hukumomin gwamnatin ƙasar.

    Ana sa ran taron zai tattauna batun yadda za a raba tallafin da za a bai wa 'yan ƙasar, don rage raɗaɗin da cire tallafin man fetur ya haddasa.

    An dai samu tashin farashin man fetur a ƙasar bayan cire tallafin, lamarin da ya ƙara ta'azzara tashin farashin kayayyaki a ƙasar.

    Shugaban ƙasar Bola Tinubu ne ya sanar da bayar da tallafin domin taimaka wa talakawan ƙasar wajen rage musu raɗaɗin da suke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur ɗin.

    Vice President Nigeria

    Asalin hoton, Kashim Shettima/Facebook

  13. Man fetur da ake sha a Najeriya ya ragu da kashi 35

    t

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA ta ce yawan man da ake amfani da shi a ƙasar a kowacce rana ya ragu zuwa lita miliyan 46.34, sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi.

    Shugaban hukumar, Ahmed Farouk, ne ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki kan harkokin albarkatun man fetur da iskar gas a birnin Legas, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN ya ruwaito.

    Ya ƙara da cewa raguwar ta kai kashi 35 cikin 100 idan aka kwatanta da lita miliyan 65 da ake amfani da shi a kowacce rana kafin cire tallafin man fetur ɗin.

    Ahmed Farouk ya ce ''a watan Janairu fabrairu, an sha mai lita miliyan 62 a kowacce rana, yayin da aka sha lita miliyan 71.4 a kowace rana cikin watan Maris, sai Afiru da aka sha lita miliyan 67.7 a kowacce rana, sai watan Mayu da aka sha lita miliyan 49.5 a kowace rana, sai kuma watan Yuli da ake shan lita miliyan 46.3 a kowace rana''.

    Shugaban hukumar ya kuma gode wa 'yan kasuwar da suka nuna sha'awarsu wajen shigar da man fetur ƙasar daga kasuwannin duniya.

    Ya kara da cewa kawo yanzu kamfanoni 56 ne suka nuna sha'awarsu wajen shigo da man fetr zuwa ƙasar, yayin da kamfanoni 10 suka zaku wajen fara shigo da man.

    Ahmed Farouk ya ce yanzu haka kamfanoni uku sun fara shigo da man fetur ɗin daga ƙasashen waje.

  14. New Zealand ta doke Norway a wasan farko

  15. Mutum ɗaya ya rasu, 48 sun jikkata a Johannesburg

    Mota

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumomi a Afirka ta Kudu kwashe mutane tare da auna irin ɓarnar da wata fashewa da ake zargin bututun gas ya haddasa a birnin Johannesburg na ƙasar.

    Rahotonni sun ce mutum guda ya sara ransa, yayin da wasu 48 suka jikkata, sakamakon fashewar da ta ahddasa rufe wasu titunan birnin.

    Hukumomin na ci gaba da gudanar da bicie domin gano abin da ya haddasa fashewar ranar Laraba da yamma.

    Jami'ai sun yi gargaɗin samun karin wata fashewar, inda suka yi kira jama'a da su kaurace wa yankin da fashewar ta auku.

    Da safiyar ranar Alhamis ne jami'ai suka sanar da rufe wasu titunan birnin domin kaucewa yankin da jami'an suka ce har yanzu yana cikin hatsari.

    Jami'an lardin Gauteng sun ce har yanzu ba a san ainihin abin da ya haddasa fashewar ba, to amma ana zargin ta afku ne sakamakon fashewar bututun iskar gas da ke ƙarƙashin ƙasa.

    Lamarin dai ya haddasa rugujewar yankin wani titi a birnin.

  16. Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga 22 a Katsina

    SOjOJI

    Asalin hoton, NAF

    Rundunar sojin sama ta Najeriya ta kashe akalla 'yan bindiga 22 a ƙananan hukumomin Jibiya da Batsari a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar.

    Jaridar PRNigeria ta ruwaito ce wa 'yan bindigar - waɗanda galibinsu yaran riƙaƙƙen ɗan bindigar nan ne da aka kashe Abdulkareem Boss - an kashe su ne ranar Litinin, a wani hari ta sama da dakarun rundunar 'Hadarin Daji' mai yaki da 'yan bindiga - a yankin arewa maso yammacin ƙasar - ta kai.

    Wata majiya mai ƙarfi a rundunar sojin ta shaida wa PRNigeria cewa an kai harin ne a kan tsaunukan da 'yan bindigar ke ɓoye, bayan samun bayan sirri da ke nuna cewa suna kitsa wani hari domin yin garkuwa da matafiya a kan hanyar Jibiya zuwa Katsina.

    Majiyar ta ce 'yan bindigar sun addabi al'umomin yankin, inda suke yin garkuwa da mazaunan wasu yankuna a ƙaramar hukumar Kankara.

    Harin wanda ya yi sanadin mutuwar 'yan bindiga da dama , ya kuma lalata sansanonin 'yan bindigar.

    A cikin watan Agustan 2022 ne dai rundunar sojin sama ta Najeriya ta kashe fitaccen ɗan bindigar nan mai suna Abdulkareem Boss tare da wasu daga cikin yaransa a wani hari ta sama da rundunar ta ƙaddamar kan maɓoyarsu a dajin Ruga da ke jihar Katsina.

    An zargi Abdulkareem da kitsi wani mummunan hari da ya yi sanadin kashe wani babban baturen 'yan sanda a ƙaramar hukumar Dutsinma ranar 5 ga watan Yulin 2022.

    Mai maganar da yawun rundunar sojin sama ta Najeriya Air Commodore Edward Gabkwet, wanda ya tabbatar da harin na ranar Litinin, ya ce babban hafsan sojin sama na ƙasar, Air Vice Marshal Hasan Abubakar, ya umarci dakarun sojin saman ƙasar da su haɗa kai da sauran jami'an tsaro domin kakkafe duka 'yan ta'addan da kuma maɓoyarsu.

  17. Gwamnonin APC sun yi taro kan saukar shugaba da sakataren jam'iyyar na ƙasa

    Gwamnonin APC

    Asalin hoton, Dr. Dapo Abiodun/Facebook

    Gwamnonin Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya sun yi ganawar sirri da maraicen ranar Laraba domin tattauna al'amuran da suka shafi jam'iyyar, bayan saukar shugaba da sakataren jam'iyyar Sanata Abdullahi Adamu da Sanata Iyiola Omisore.Iyiola Omisore.

    Saukar mutanen biyu, ya sanya nan take jam'iyyar ta sanar da naɗin mataimakain shugaban jam'iyyar na yankin arewacin ƙasar Sanata Abubakar Kyari a matsayin shugaban riƙo na jam'iyyar.

    Taron gwamnonin, ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar gwamnonin APC Sanata Hope Uzodinma, ya samu halartar gwamnonin jihohin Ekiti da Ebonyi da Niger da Benue da Kaduna da Legas da Yobe da Katsina da Kebbi da muƙaddashin gwamnan jihar Ondo, kamar yadda Gidan Talbijin na Channels TV ya ruwaito.

    A ranar litinin ne dai kwamitin gudanarawar jam'iyyar ya tabbatar da nadin Sanata Kyari a matsayin shugaban riƙo na jam'iyyar.

    A shekarar da ta gabata ne aka zaɓi Sanata Abdullahi Adamu a matsayin shugaban jam'iyyar, a babban taron da jam'iyyar ta gudanar a Abuja babban birnin ƙasar.

  18. Wagner za ta ci gaba da ayyukanta a Afirka - Prigozhin

    e

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Kamfanin sojojin hayar Rasha 'Wagner' Yevgeny Prigozhin ya shaida wa gidan talbijin na 'Afrique Media TV' cewa sojojinsa za su ci gaba da ayyukansu a inda suke a yanzu a ƙasashen Afirka

    "Za mu ci gaba da gudanar da ayyukanmu a duka ƙasashen da muka fara ayyukanmu'' kamar yadda ya bayyana.

    Ya ƙara da cewa "Duk ƙasar da ta buƙaci taimakon ƙungiyar Wagner a ko'ina domin yaƙar 'yan tawaye da 'yan ta'adda, za mu taimaka domin kare 'yan ƙasar da zarar an amince da sharuɗa da aƙa'idojinmu''.

    Mista Prigozhin ya ce ƙungiyar ba ta da niyyar rage ayyukanta a Afirka.

    Kalaman nasa na zuwa ne bayan samun raɗe-raɗin janye dakarun ƙungiyar daga ƙasashen Mali da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka, bayan taƙaitaccen boren da ƙungiyar ta yi a Rasha ranar 24 ga watan Yuni.

    Kungiyoyin kare hakkin bil-adama na zargin dakarun Wagner da keta hoƙƙokin bil-adama a Mali da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka.

  19. An kashe mutum biyu a New Zealand gabanin fara gasar Kofin Duniya ta Mata

    'Yan sanda

    Asalin hoton, Reuters

    An kai wani hari birnin Auckland na kasar New Zealand, sa'o'i gabani fara gasar Kofin Duniya ta Mata a birnin.

    Harin - da wani ɗan bindiga ya kai ya raunata mutum shida, ciki har da 'yan sanda.

    Daga baya shi ma maharain ya mutu a wani waje da ake gini a tsakiyar birnin.

    Firaministan kasar Chris Hipkinsya ce harin bai yi kama da na ta'addanci ba, ya kuma tabbatar da cewa za a ci gaba da gasar Kofin Duniyar ta Mata kamar yadda aka tsara ta.

    Tuni dai aka take wasan tsakanin mai masaukin baki New Zealand da kasar Norway.

    Yayin da babu wani da ko wata kungiya da ta ɗauki alhakin harin, firaministan kasar ya ce 'yan sanda sun tabbatar wa al'umma cewa babu wani sauran barazana.

    Magajin garin birnin Auckland Wayne Brown ya ce harin ba shi da alaƙa da gasar Kofin Duniya ta Mata da ƙasar ke ɗaukar baƙunci.

  20. Sallama

    Masu bin mu a wannan shafi barkan mu da safiyar ranar Alhamis, da Hausawa ke yi wa kirari da ta Bawa ranar sanar samu.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kun wayi gari lafiya, tare da fatan kasancewa da ku a wannan yini domin kawo muku irin labaran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman Najeriya da makwabtan ƙasashe.

    Kuna iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.

    Ku biyo mu....