Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Bayanai da martani kan dage zaben Najeriya

Wannan shafi na kawo muku labarai da rahotanni da bayanai har ma da martani kan matakin da hukumar zaben Najeriya ta dauka na dage zaben.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahya and Mohammed Abdu

  1. Nan muka kawo karshen shirin da fatan za ku tara nan gaba.

    Nine Nasidi Adamu Yahaya tare da Mohammed Abdu Mamman Skeeper mu muke ce muku sai anjima.

  2. Kananan 'yan kasuwa na gudanar da kasuwanci

    Kananan 'yan kasuwa sun ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a Makurdi, bayan da hukumar zabe ta Nigeria ta dage zaben da ta shirya gudanarwa.

  3. Rochas ya yi bayani kan daga zabe

    Gwaman jihar Imo Rochas Okorocha ya yi bayani kan daga wannan zabe

  4. Matsalolin da za a iya fuskanta bayan dage zabe

  5. Muna gabatar da labarai kai tsaye a radiyo

  6. 'APC da fadar Buhari ne suka sa aka dage zabe'

    Jam'iyyar hamayya a Najeriya, PDP, ta yi zargin cewa jam'iyyar APC mai mulki da fadar shugaban kasar ne suka kitsa dage zaben Najeriya domin bai wa shugaban kasar damar magudin zabe, tana mai cewa 'yan Najeriya ba za su amince da duk wani yunkurin magudi ba.

  7. Atiku zai koma Abuja, bayan dage zabe

    Dan takarar shugaban Najeriya na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya kama hanyarsa ta komawa Abuja inda zai yi taro da masu ruwa da tsaki na jam'iyyarsa da kuma sauran jama'a kan dage zaben da INEC ta yi.

  8. INEC na shirin yi wa masu sa ido jawabi

    Hukumar zaben Najeriya ta shirya tsaf domin yi wa masu sanya ido na kasashen waje kan zaben kasar jawabi kan dalilanta na dage zabukan 2019.

  9. Dage zabe: Me ya sa 'yan Najeriya ke son komawa Canada?

    Tun bayan da hukumar zaben Najeriya ta sanar da dage manyan zabukan kasar, masu mu'amala da shafukan sada zumunta musamman Twitter a kasar suka soma aike wa da sakonni da ke nuna shaukinsu na son komawa kasar Canada.

    Sakonnin sun kunshi na ban dariya da ban haushi da gatsine.

  10. Buhari ya garzaya Abuja

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya garzaya Abuja daga Katsina. Sanarwar da ya fitar ta ce shugaban ya yanke shawarar komawa Abuja ne saboda ya tabbatar cewa taron da hukumar zabe za ta gudanar da masu ruwa da tsaki ya yi nasara.

  11. Martanin kungiyar tuntuba ta Arewa Consultative Forum

    Kungiyar tuntuba ta ‘yan arewa mai nsuna Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana takaicinta na dage babban zabe da Hukumar Zaben Najeriya ta yi.

    Kungiyar ta ce dagewar ya kamata a ce an yi ta tun a baya domin a rage wa ‘yan kasa da sauran wadanda abin ya shafa wahalhalu.

    “Shirye-shiryen da INEC ta ce ta yi ya kara wa ‘yan Najeriya kwarin gwiwa game da samun cikakken zabe na adalci. ACF da ‘yan Najeriya ba su da wani zabi face su ci gaba da fatan INEC ta cika alkwarainta na zabe mai adalci.’

  12. Ra'ayoyin mutane daga Makurdi kan dage zabe

  13. Ra'ayoyin mutane daga Kano kan dage zabe

  14. Ra'ayoyi daga shafin Twitter

  15. Buhari ya bayyana rashin jin dadinsa game da dage zabe

    A bayanan da ya wallafa a shafinsa na Twitter, shugaban ya shawarci ‘yan Najeriya da su kauce wa tashin hankali.

    Ya kuma ce zai dawo Abuja domin ci gaba da ayyukan gwamanti.

    Na yanke shawarar dawowa Abuja domin halartar ganawa da INEC ta shirya gudanarwa da masu-ruwa-da-tsaki da karfe 2 na rana.

    “Ina shawartar ‘yan Najeriuya da su guje wa taashin hgankali kuma su bzama ‘yan kasa na garidomin kada su kawo wa dimokradiyyar Najeriya nakasu.”

  16. Tattaunawa kan dage zaben Nigeria da aka yi

  17. Yadda muke gabatar da shirye-shirye a radiyo

    Shirin safe da muka gabatar kai tsaye a radiyon BBC.

    Sakamakon dage zaben da aka yi mun tsara kawo muku shirin awa daya da rana da kuma shirin maraice.

  18. 'Yadda 'yan jarida suke jiran jawabin Atiku Abubakar

    'Yan jarida da dama ne suka yi shirin daukar labarin yadda tsohon mataimakin shugaban Nigeria, Atiku Abiubakar zai yi zabe a Jada jihar Adamawa, Nigeria.

    Sai kuma hukumar zabe ta ce ta dage zaben.

  19. Wasu 'yan kasuwa sun fara gudanar da kasuwanci

    'Yan kasuwar kayan miya inda akafi sani da ramin Kura a cikin garin Sokoto,sun fito sun ci gaba da sana'ar su, bayan dage zabe.

  20. Wasu ra'ayoyi daga shafin Twitter