Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labarin wasanni daga 20 zuwa 26 ga watan Disamba 2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Asabar 13 zuwa 19 ga watan Disambar 2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Liverpool ba za ta shiga ƴan huɗu ba saboda cinta da ake ta kwana da bugun tazara, Arne Slot

    Arne Slot ya ce da ƙyar Liverpool ta shiga ƴan huɗun farko a teburin Premier League, sakamakon cin da ake musu ta kwana da bugun tazara da kuma jifa.

    Ƙungiyar Anfield tana mataki na biyar a teburi da maki iri ɗaya da na Chelsea, bayan da za a ci gaba da wasannin mako na 18 daga karshen mako.

    An ci Liverpool ƙwallo 11 daga bugun ko dai kwana ko na tazara ko kuma jifa, yayin da ta ci uku.

    Haka kuma Liverpool na fama da masu jinya, bayan da Alexander Isak zai yi jinyar watanni, saboda raunin da ya ji a gidan Tottenham a Premier League.

    Slot na fatan Cody Gakpo da kuma Conor Bradley za su murmure, domin buga wa Liverpool wasan da za ta buga da Wolverhampton.

    Mohamed Salah yana buga wa Masar gasar Afcon, yayin da Wataru Endo ke jinya, sannan an dakatar da Dominik Szoboszlai.

  2. Chelsea za ta fara wasan Aston Villa da Palmer a Premier

    Kocin Chelsea, Enzo Maresca, ya ce zai fara wasan da za su buga da Aston Villa da Cole Palmer a gasar Premier League ranar Asabar, bayan watanni da ya shafe yana jinya

    An takaita sa Palmer a wasanni, bayan da yake kokarin komawa kan ganiya, bayan kammala jinya.

    “Ina ganin (Palmer) ya shirya buga mintuna 90. Ya fara da buga mana mintuna 45 da kuma awa ɗaya, sannan ya yi mana minti 70,” in ji Maresca a lokacin da ya gana da ƴan jarida kan wasan da za su kara ranar Asabar.

    “Ya riga ya buga awa ɗaya a wasabEverton da yin fiye da mintuna 70 a karawa da Newcastle, don haka ina ganin zan iya fara wasan Aston Villa da shi.”

    Kocin ɗan Italiya zai kuma yi maraba da dawowar wasu ƴan wasa biyu daga jinya, inda Liam Delap ya murmure daga raunin kafaɗa, sannan Estevao ya dawo daga raunin da ya hana shi buga wasanni biyu da suka gabata.

  3. Howe ya ce zai fuskanci kalubale a Man United ranar Juma'a, Manchester United da Newcastle United

    Eddie Howe ya gargadi ’yan wasansa na Newcastle United cewa rinjayen da suka yi a baya a kan Manchester United ba zai yi musu wani amfani ba a wasan da za su buga a Old Trafford ranar Juma'a.

    Newcastle United za ta je wasan ne bayan da ta yi nasara a karawa biyar daga shida a baya bayan nan da ta fafata da United a dukkan karawa, da kuma huɗu daga biyar a wasannin Premier League, tun bayan da suka sha kashi 2-0 a hannun Red Devils a wasan ƙarshe a Carabao Cup 2023.

    Newcastle ta kammala kakar da ta gabata a matsayi na 10 a teburi sama da Manchester United kuma da maki 24 tsakani, amma za ta Old Trafford da tazarar maki uku tsakani da mai masu masaukin baki,

    Ƙungiyar St James Park ta ɓarar da maki biyu a makon jiya, bayan da ta fara cin Chelsea ƙwallo biyu daga baya suka tashi 2-2 a gasar ta Premier League.

    Sabon ɗan wasan da ta saya da farashi mafi tsada, Nick Woltemade ne, ya ci ƙwallayen biyu.

    United tana mataki na bakwai a kan teburin Premier League da maki 26, ita kuwa Newcastle mai maki 23 tana ta 11.

  4. Eisa na fatan Afcon da za su yi zai saukaka yaƙin basasa a kasar, Sudan

    Ɗan wasan Sudan, Abobaker Eisa, ya ce yana fatan buga gasarcin kofin Afirka da za su yi a Morocco zai kawo karshen yaƙin basasar kasar.

    Tun daga watan Afrilu 2023, Sudan na cikin halin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana a matsayin mafi girman rikicin jin ƙai a duniya, bayan faman neman iko tsakanin sojojin ƙasa da wata rundunar sa-kai mai ɗauke da makamai, Rapid Support Force (RSF), ya rikide zuwa yaƙi.

    Fiye da mutane 150,000 ne suka rasa rayukansu, yayin da sama da miliyan 12 aka tilasta musu barin gidajensu, tare da yaɗuwar yunwa da kuma rahotannin kisan kare dangi a yankin Darfur ta Yamma.

    Rikicin ya tilasta wa Sudan buga dukkan wasannin neman tikitin gasar a wajen kasar, amma duk da haka ta samu nasarar shiga wasannin da aka fara a Morocco, kuma karo na huɗu tun 1976.

    Zakarun gasar a 1970 za su fafata da Algeria ranar Laraba 24 ga watan Disamba da fuskantar Equatorial Guinea ranar 28 ga ga watan Disamba da kuma wasan karshe a cikin rukuni da Burkina Faso ranar 31 ga watan Disamba.

    Eisa ya ce babbar gasar cin kofin Afirka “babban al’amari ne” kuma wata hanya ce ta kawar da hankalin mutanen Sudan daga halin da ƙasar ke ciki.

  5. Watakila Man City ta ɗauki Semenyo a watan Janairu, Manchester City

    Ana sa ran Antoine Semenyo zai yanke shawara ta ƙarshe kan makomarsa, yayin da Manchester City ke cikin tattaunawa kan yiwuwar ɗaukar ɗan wasan Bournemouth da zarar an buɗe kasuwar sayen ƴan ƙwallo ta watan Janairu.

    A cewar majiyoyi, City ta samu ƙwarin gwiwa a ƴan kwanakin nan kan shirin ɗaukar ɗan wasan mai shekaru 25.

    Majiyoyi sun kara da cewar wasu ƙungiyoyi huɗu na Premier League ma suna tambayar makomar ɗan ƙwallon, ta hanyoyi daban-daban, game da Semenyo, wanda ke da yarjejeniyar fam miliyan 65 (£65m).

    Ana fahimci cewar waɗannan ƙungiyoyin su ne Manchester United da Liverpool da Tottenham da kuma Chelsea.

    Sai dai Manchester United ta janye daga cikin masu zawarcisaboda tana tsammanin Semenyo zai koma ƙungiyar da Pep Guardiola ke horarwa, yayin da Chelsea ta yanke shawarar kin ci gaba da neman ɗan wasan.

  6. Napoli na fatan kara lashe Serie A, bayan Italian Super Cup, Antonio Conte

    Bayana da ta lashe Italian Super Cup, Napoli za ta ci gaba da fafatawa domin kare kofin Serie A, wadda take da kwarin gwiwa a shirin da take na zuwa gidan Cremonese a karshen mako.

    Napoli ta yi nasarar doke AC Milan 2-0 a daf da karshe da cin Bologna 2-0 da ta kai ta ɗauki Super Cup a karon farko tun bayan 2014, bayan da Antonio Conte ke kara ɗaukar wa ƙungiyar kofuna.

    Conte ya fara da lashe Serie A a kakarsa ta farko a Napoli.

  7. ''Mozambique na san taka rawar gani a Afcon'', Mozambique

    Ƙasar Mozambique na fatan za ta iya fuskantar kalubalen da aka jefa ta ciki da fatan za ta kai zagaye na biyu a gasar AFCON ta 2025, a cewar tsohon ɗan wasanta, Manuel Bucuane.

    Mambas ba ta taɓa wuce matakin rukuni ba a kaka biyar da suka yi a baya, kuma har yanzu tana fatan samun nasara ta farko a wasannin Afcon, bayan da ta yi kunnen doki biyar kuma ta sha kashi karo 10 daga wasa 15 da ta buga a baya a gasar ta cin kofin Afirka.

    Tawagar da Chiquinho Conde ke jan ragama an jefa ta rukuni na shida mai ɗauke da mai rike da kofin Ivory Coast, da wadda ta lashe kofin karo biyar, Kamaru da kuma Gabon wadda Pierre-Emerick Aubameyang ke jagoranta. Duk da haka, Bucuane yana da kyakkyawan fata.

    Mozambique ta samu tikitin shiga wasannin gasar karo na biyu a jere a karon farko tun 1998, bayan da ta yi kunnen doki da Masar da Ghana a gasar AFCON a 2023 da aka yi a Ivory Coast.

  8. Wasannin da za a buga a Afcon ranar Laraba, Afcon 2025 Morocco

    Rukuni na biyar:

    • Burkina Faso da Equatorial Guine
    • Aljeriya da Susan

    Rukuni na shida:

    • Ivory Coast da Mozambique
    • Kamaru da Gaban
  9. Mbeumo zai buga wa Kamaru Afcon a karon farko

    Ɗan wasan Kamaru, Bryan Mbeumo, ya ce yana cike da farin ciki gabanin wasan farko da zai buga wa kasar a gasar cin kofin Afirka da ake yi a Morocco,

    Ɗan wasan da ke taka leda a Manchester United bai halarci wasannin da aka yi a Ivory Coast ba, sakamkon jinya.

    Tawagar Kamaru za ta kece raini da ta Gabon ranar Laraba a karawar rukuni na shida da ya haɗa da mai rike da kofin, Ivory Coast da kuma Mozambique.

    Da yake magana da CAFOnline a sansanin horon Indomitable Lions a Agadir, ya bayyana farin cikinsa na samun damar shiga babbar gasar ƙwallon ƙafa ta Afirka a karon farko.

    “Gaskiya ina matuƙar farin ciki. Na daɗe ina jiran wannan lokaci, kuma ina matuƙar farin ciki da zan wakilci kasata a nan Moroko,” in ji Mbeumo.

    Tsohon ɗan wasan Brentford, wanda ya riga ya wakilci Kamaru a Kofin Duniya a 2022, ya kwan da sanin irin muhimmancin da gasar AFCON take da shi a fannin tamaula.

    Kamaru ta shiga gasar a matsayin ɗaya daga cikin tawagar da ake sa ran za ta kai zagaye na biyu kai tsaye. Sai dai Mbeumo ya ce ba ya jin matsi kan gasar, duk da dimbin tarihin nasarar Kamaru a AFCON.

    Ɗan wasan, wanda ya ci ƙwallo shida a wasa 16 a Premier League a kakar bana, ya jaddada irin fatan da koci, David Pagou ke da shi a kansa, yayin da yake sa ran taka muhimmiyar rawa ga Indomitable Lions.

    Ana sa ran Mbeumo zai kasance ɗaya daga cikin ƴan wasan da za a fi sa ido a kansu ga Kamaru a gasar, yayin da Indomitable Lions ke ƙoƙarin komawa kan ganiya a ƙwallon ƙafa na nahiyar Afirka, mai Afcon biyar.

  10. Chelsea ba za ta yi zawarcin Semenyo a watan Janairu ba

    Chelsea ta yanke shawarar janye wa daga zawarcin Antoine Semenyo, yayin da ɗan wasan Bournemouth ya fara tunanin makomarsa a ƙungiyar.

    Tun farko Chelsea ta yi binciken damar dayen ɗan wasan mai shekaru 25, amma ba za ta ci gaba da neman sa ba.

    Wasu majiyoyi sun shaida wa BBC cewa ƙungiyoyi huɗu ma sun nuna sha’awa ɗaukar Semenyo, ta hanyoyi daban-daban, gabanin buɗe kasuwar sayen ƴan wasa a watan Janairu.

    An fahimci cewa waɗannan ƙungiyoyin su haɗa da Manchester City da Manchester United da Liverpool da kuma Tottenham.

    Ƙungiyoyin birnin Manchester biyu ne ake ganin sun fi nuna sha'awar sayen ɗan ƙwallon.

    Musamman Manchester City, a cewar majiyoyi ta samu ci gaba a ƴan kwanakin nan kuma tana kan matsayi da za ta iya ɗaukar Semenyo.

    Liverpool ma na son shiga cikin ɗan wasan, amma har yanzu ba ta nuna cewar ko za ta taya shi a watan Janairu ba, bayan da Salah ya je buga Afcon, Isak ya ji rauni Gapko na jinya.

    Amma dai Tottenham ba ta nuna karara cewar sai ta ɗauki ɗan wasan tawagar Ghana, wanda ya koma Bournemouth a shekarar 2023 daga Bristol City.

    Semenyo yana da yarjejeniyar fam miliyan 65 (£65m).

  11. Wasannin Premier League a karshen mako, Premier League mako na 18

  12. Guardiola ya ja kunnen ƴan wasa su kasance kan ganiya, Pep Guardiola

    Kocin Manchester City ya sanar cewa duk ɗan wasan da ya dawo daga hutun bukukuwan ƙarshen shekara ba tare da yana kan ganiya ba, ba zai shiga wasan da za su yi da Nottingham Forest a mako mai zuwa ba.

    Guardiola ya ƙi bai wa ƴan wasansa hutu bayan nasarar da suka samui a wasan Premier League da West Ham a ranar Asabar, domin tabbatar da cewa saƙon ya isa kunnensu.

    Kocin ɗan Sifaniya bai gamsu da matakin wasan da aka buga ba, duk da cewa sun yi nasarar cin 3-0 — duk da cewa ita ce nasara ta biyar a jere a gasar — City na ci gaba da matsa lamba kan Arsenal, wadda ke kan tebur Premier League.

  13. Slot ya zargi Van de Ven da ya yi wa Isak mummunar keta, Liverpool

    Kocin Liverpool, Arne Slot, ya soki ɗan wasan Tottenham Micky van de Ven kan keta mai muni da ya yi, wanda ya jawo ɗan wasan Alexander Isak ya ji rauni zai kuma yi jinyar watanni sakamakon karya kafa da ya yi.

    Ɗan wasan Sweden ɗin ya ji rauni ne a lokacin da ya ci ƙwallon farko a wasan da suka dke Tottenham 2-1 ranar Asabar.

    Ranar Litinin aka yi wa Isak tiyata, daga nan aka fayyace zai yi jinyar watanni kafin ya koma taka leda.

  14. Wolves ta yanki tikitin barin Premier League a bana

    Ƙungiyar Wolves na dab da faduwa daga gasar Premier League a bana, bayan da ta sha kashi karo na 10 a jere, sakamakon rashin nasarar 2-0 a hannun Brentford.

    Hakan ya sa ta zama ƙungiya ta huɗu a tarihin Premier League da ta taɓa yin rashin nasara a wasa 10 a jere cikin kakar wasa ɗaya.

    Yanzu tana fuskantar kalubalen karawa da Liverpool a gasar Premier League.

  15. Rangers ta samu kwarin gwiwa bayan da Souttar ya warke

    Ƙungiyar Rangers ta samu labari mai daɗi a bangaren tsaron bayanta, bayan da John Souttar ya koma atisaye a wannan makon.

    Mai tsaron bayan tawagar Scotland ɗin bai yi wasa takwas da suka gabata sakamakon jinya, hakan ya sa koci, Danny Rohl ya fuskanci kalubale a gurbin masu tsare baya, saboda Derek Cornelius ma na jinya, yayin da Nasser Djiga ke Morocco buga gasar AFCON.

    Sai dai da kyar ne idan Souttar zai iya fuskantar Motherwell a babbar gasar tamaula ta Scotland ranar Asabar.

    Amma za a iya fara karawar da Rangers za ta yi da St Mirren a ranar 30 ga watan Disamba.

  16. Haaland na kishirwar cin ƙwallaye a duk wasa - Gvardiol, Manchester City

    Josko Gvardiol ya ce babu yadda za a taɓa kosar da Erling Haaland game da sha’awarsa ta cin ƙwallaye da ke cikin ransa a kowane wasa.

    Fitaccen ɗan wasan gaban, ya ci ƙwallaye 25 a wasa 23 da ya buga wa Manchester City a kakar bana, lamarin da yake da jimillar 149 daga wasa 189 tun bayan da ya koma Etihad a 2022.

    Ƙwallaye biyu da ya ci wa City da ta doke West Ham 3-0 a ranar Asabar, ya sa suna mataki na biyu a teburin Premier League da tazarar maki biyu tsakani da Arsenal mai jan ragama.

    “Ina fatan zai ci gaba da sa kwazo,” in ji mai tsaron baya Gvardiol. “Gare shi, ina ganin ba ya taɓa gamsuwa da cin ƙwallaye. A bayyane hakan yake, yana son ya ci ƙwallaye a kowane wasa, aƙalla guda biyar.

    City za ta buga wasan mako na 18 a gasar Premier League ranar Asabar a gidan Nottingham Forest.

  17. Afcon: Ko Super Eagles za ta doke Tanzania a wasan farko a rukuni?, Afcon Morocco 2025

    Tawagar Najeriya da ta Tanzania za su kara a gasar cin kofin Afirka wasan farko a rukuni na uku a karo na biyu kenan a babbar gasar tamaula ta Afirka tun bayan shekara 45.

    Sun fara haduwa a AFCON a 1980 lokacin da Najeriya ta shirya wasannin, wadda ta fara karawar farko da doke Tanzania 3-1 a Legas ranar 8 ga watan Maris 1980. Kuma shi ne kofin farko da ta lashe.

    Amma kuma jimilla sun fafata a tsakaninsu karo bakwai a dukkan haduwa, inda Najeriya ta yi nasara hudu da canjaras uku, sannan Najeriya ta ci kwallo 11, ita kuwa Tanzania ta zura mata uku kacal.

  18. Ko ya kamata Liverpool ta shiga kasuwa bayan da Isak ya ji rauni?, Liverpool

    Shin raunin da Alexander Isak ya samu na nufin ya kamata Liverpool ta shiga kasuwar sayen ’yan wasa?

    Mohamed Salah yana buga gasar AFCON tare da Masar, yayin da Cody Gakpo har yanzu ke jinya, don haka nauyin cin ƙwallaye ya rataya a wuyan Hugo Ekitike, amma ba zai iya buga kowane minti na kowane wasa ba.

    Rahotanni sun nuna cewa an danganta Liverpool da ɗan wasan gefen Bournemouth, Antoine Semenyo, amma da alama kusan duk manyan kungiyoyi ma suna sha’awar sayensa.

  19. Jamhuriyar Congo ta fara da cin Benin a Afcon

    Jamhuriyar Congo ta fara buga gasar cin kofin Afirka da kafar hagu, bayan da ta ci Benin 1-0 a wasan farko a rukuni na uku da suka kara a Rabat

    Tawagar da ake kira The Leopards ta ci ƙwallon a minti na 16 ta hannun Theo Bongonda daga yadi na 10.

    Ana sa ran Senegal za ta iya samun maki uku a ɗaya wasan rukunin da za ta kara da Botswana a daren nan a fafatawar rukuni na huɗu.

  20. An fitar da Sriram Balaji daga tawagar India a Davis Cup

    Kwamitin zaɓen AITA a ranar Talya cire N. Sriram Balaji daga cikin tawagar da za ta fafata a gasar Davis Cup mai zuwa da Netherlands, amma sauran ƴan wasan ba awanda aka taɓa..

    Za a buga wasan zagayen farko a Bengaluru a ranakun 7 da 8 ga Fabrairun 2026.

    Sumit Nagal ne zai jagoranci ƙalubalen wasannin Indiya, yayin da tawagar ta kuma ƙunshi ƙwararren ƴan wasan da ya haɗa da Yuki Bhambri, tare da Dhakshineswar Suresh da Karan Singh.

    Ƴan wasan tawagar: Sumit Nagal, Dhakshineswar Suresh, Karan Singh, Yuki Bhambri da kuma Rithvik Bollipalli.

    Masu jiran ko-ta-kwana: Aryan Shah, Anirudh Chandrashekhar da kuma Digvijay Singh.